Masana’antar shirya fina-finai ta kasar Sin ta kafa wani sabon tarihi a hutun bikin bazarar 2025, inda daga ranar 29 ga watan Janairu zuwa ranar 1 ga Fabrairu, kudaden da aka samu daga kallon fina-finai ya kai biliyan 5.75 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 802, wanda ya zarce mafi yawan kudin da aka samu a baya na yuan biliyan 5.

73 a shekarar 2021. 

Wannan adadi shi ne mafi yawan kudi da aka samu daga kallon fina-finai a lokacin bikin bazara a tarihin sinima ta kasar, kuma ya tabbatar da matsayin kasar Sin na kasancewa jagora wajen samun mafi yawan kudade daga kallon fina-finai wato box office a shekarar 2025, wanda ya zarce Arewacin Amurka.

Gwamna Buni Ya Jaddada Bai Wa Sojoji Gudunmawar Kawo Karshen Boko Haram  An Kammala Aikin Tsugunar Da Mutane A Gundumar Tingri Ta Sin Bayan Bala’in Girgizar Kasa

Bisa al’ada bikin bazara kololuwar lokaci ne na zuwa kallon fina-finai da samun riba ga masu shirya fina-finai, an samu zazzafar gasa tsakanin manyan fina-finai da aka saki. An kuma tsawaita hutun bikin bazara da kwana daya zuwa kwanaki takwas a wannan shekara, wanda ke gudana daga ranar 28 ga Janairu zuwa 4 ga Fabrairu.

Carton mai sun “Ne Zha 2” ne ke kan gaba a jerin manyan shirye-shirye, wanda ya samu sama da yuan biliyan 2.3 a cikin kwanaki hudu kacal, a cewar bayanan da kafar Beacon mai bibiyar fina-finan box office ya fitar. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa

Rundunar ‘Yansandan Jihar Adamawa ta kama Umar Shaibu bisa zargin cin zarafin wata mata a yankin Jimeta a jihar. An kama Shaibu ne bayan wani bidiyo mai tayar da hankali ya yadu a kafafen sada zumunta, kamar yadda Jami’in hulda da Jama’a na ‘Yansandan Jihar Adamawa, SP Suleiman Nguroje, ya bayyana. Salamatu Yakubu, matar mai shekaru 22 daga Angwan Tana, an ce wanda ake zargin ya yi ma ta dukan jakin ne mai tsanani, Shaibu, wanda ake cewa shi ne dan uwanta.

Wannan lamarin ya janyo zarge-zargen daga al’umma da kuma kiran da aka yi wa Yansanda daga mutanen gari, da kungiyoyin fararen hula, da sauran masu rajin kare hakkin bil’adama domin a kama wanda ake zargi.

Ƴansanda Sun Kama  Ɓarayin Waya Masu Amfani Da Keke Napep A Adamawa An Kama Wanda Ake Zargi Da Kashe Mai PoS A Adamawa

An kama Shaibu ne tare da taimakon al’umma ta hanyar dabarun kula da tsaro na cikin gari. An tura matar da aka yi wa dukan cutar zuwa asibiti domin samun kulawar likita.

A halin yanzu, wanda ake zargin yana tsare a sashin binciken laifuka na musamman na Jihar (SCID) a sashin kula da mata domin a gudanar da cikakken bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu. Rundunar Yansandan ta tabbatar wa da jama’a cewa za a binciki lamarin sosai kuma wanda ake zargi zai fuskanci shari’a bisa dokokin da suka dace.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UEFA: Mbappe Zai Jagoranci Real Madrid Yayin Da Ta Ke Fatan Kafa Sabon Tarihi A Santiago
  • Yadiot Ahranot: Amurka Ta Bayyana Lokacin Ficewarta Daga Syria
  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
  • Jagoran Ya Ce: Iran Ba Ta Kallon Tattaunawan Iran Da Amurka A Matsayin Kawo Karshen Takaddama A Tsakaninsu
  • ’Yan Najeriya sun koka kan rashin ingancin shinkafar Gwamantin Tarayya
  • Jama’a sun koka kan rashin inganci shinkafar Gwamanti a Kogi
  • Kamata Ya Yi Amurka Ta Kara Kokarin Gyara Kuskurenta 
  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19