Leadership News Hausa:
2025-03-24@16:51:47 GMT

Arsenal Ta Nunawa City Kwanji A Emirates

Published: 2nd, February 2025 GMT

Arsenal Ta Nunawa City Kwanji A Emirates

Arsenal ta doke Manchester City a wani yanayi mai ban mamaki a filin wasa na Emirates dake birnin Landan, ƙwallaye da Odegaard, da Partey, da Skelly, da Harvertz da Nwaneri suka jefa ya sanya Man City cikin garari.

Tun minti na 2 da fara wasan kyaftin ɗin tawagar Arsenal Martin Ordegaard ya jefa ƙwallo a ragar Manchester City bayan da ɗan wasan baya Nathan Ake ya tafka kuskure.

Juma Bah: Balladolid Za Ta Kai Manchester City Kara Gaban Kotu Arsenal Ta Matsawa Liverpool Ƙaimi Bayan Doke Tottenham A Emirates 

Duk da ƙwallon da Haaland ya ci bai hana Arsenal raga raga da City a wasan mako na 24 na gasar Firimiyar  ba, wannan sakamakon ya sanya magoya bayan ƙungiyar sa rai wajen lashe kofin Firimiya gasar ta bana.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arsenal

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet

Jagoran ‘yan adawar Isra’ila Yair Lapid ya yi kira da a gudanar da zanga-zangar gama-gari idan Firaministan kasar Benjamin Netanyahu ya ki bin hukuncin da kotun kolin kasar ta yanke na dakatar da matakin da gwamnatinsa  na korar shugaban hukumar tsaron cikin gida ta Shin Bet.

 Yair Lapid ya shaidawa dubban masu zanga-zanga a Tel Aviv cewa “Idan har gwamnatin 7 ga watan Oktoba ta yanke shawarar kin yin biyayya ga hukuncin kotun, to za ta zama haramtacciyar gwamnati a wannan rana.”

“Dole ne tattalin arzikin kasar ya tsaya cik, majalisa ta shiga yajin aiki, kotu ta shiga yajin aiki, hukumomi su shiga yajin aikin, ba jami’o’i kadai ba, har da makarantu.” Inji shi.

A ranar Juma’a ne Kotun kolin Isra’ila ta dakatar da matakin da gwamnati ta dauka na korar shugaban Shin Bet, Ronen Bar, wanda ba a taba ganin irinsa ba, wanda sanarwar korar tasa ta sake haifar da baraka a tsakanin al’umma.

Amma Netanyahu ya dage kan cewa,”Ronen Bar ba zai ci gaba da zama shugaban Shin Bet ba, ba za a yi yakin basasa ba, kuma Isra’ila za ta ci gaba da kasancewa a matsayin kasa ta dimokuradiyya,” in ji shi a cikin wani sakon bidiyo inda yake kalubalantar Kotun Koli.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yaushe Ronaldo Zai Daina Jefa Kwallo A Raga?
  • Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi
  • Wata mata ta haifi jaririn da ba nata ba
  • Iran da Masar sun tattauna kan rikicin da Isra’ila ta jefa yankin gabas ta tsakiya
  • Ko Raunin ‘Yan Wasa Zai Rage Wa Barcelona Karsashi A Kakar Bana?
  • Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!
  • An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
  • An yi wa wata karya tiyatar ceton rai
  • Chelle Ya Fara Da Ƙafar Dama A Super Eagles