Leadership News Hausa:
2025-03-25@17:41:29 GMT

Ƴansanda Sun Daka Wasoso Kan Gungun Ƴan Daba A Kano 

Published: 3rd, February 2025 GMT

Ƴansanda Sun Daka Wasoso Kan Gungun Ƴan Daba A Kano 

Rundunar Ƴansandan jihar Kano ta cafke wasu matasa a yankin Sheka bayan ɓarkewar rikici tsakanin ƙungiyoyin ƴan daba.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Kiyawa, ya bayyana hakan a shafinsa na Facebook, yana mai cewa rikicin ya fara ne bayan mutuwar wani matashi mai suna Yusuf Aminu, ɗan unguwar Sheka Babban Layi, wanda ake zargi da aikata fashi da sauran laifuka.

Dabaru Irin Na Sin A Kan Daidaita Harkokin Duniya A 2024 An Yi Taro Don Tattauna Dabarar Aiwatar Da Shawarar Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya A MDD

Rahotanni sun nuna cewa marigayin mamba ne na ƙungiyar ‘Yan Shida,’ wacce ta addabi yankin Sheka da aikata fashi da tashin hankali. Wasu mazauna unguwar sun kama shi, suka kakkarya masa ƙafa tare da jikkata wasu, wanda hakan ya kai ga mutuwarsa.

Bayan faruwar lamarin, abokan marigayin suka yi ɗamarar ɗaukar fansa, lamarin da ya janyo rikici mai muni a yankin. Sai dai ‘yansanda sun yi gaggawar shiga tsakani, suka kama wasu daga cikin matasan tare da maido da doka da oda a yankin.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya

A gobe Litinin 24 ga watan Maris ne tawagogin masu tattaunawa na kasashen Amurka da Rasha zasu hadu a birnin Rayida na kasar Saudiya don ci gaba da tattaunawan da suka fara a yan makonnin da suka gabata dangane da yakin da ke faruwa a Ukraine, shekaru fiye da 3 da suka gabata, da kuma dangantaka a tsakanin kasashen biyu.

Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto Yury Ushakov mai bawa shugaba Putin shawara kan al-amurin siyasa yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa Sanata Georgy Karasin ne zai jagoranci tawagar masu tattaunawa ta kasar Rasha sannan ta kasar Amurka an rika an samar da tawagar, wasu zata hadu da na Rasga a gobe litin a birnin Riyad.

Kafin haka dai shugaban kasar Rasha Vladimir Putin sun tattauna da tokwaransa na kasar Amurka Donal Trump kan al-amura da dama wadanda suka shafi yakin a Ukraine da tsagaita budewa juna wuta na wata guda da kuma wasu al-amura.

Karsin daga karshe ya ce yana fatan tattaunawan zata yi armashi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe
  • Za mu ɗauko hayar sojojin ƙetare domin horas da dakarun Nijeriya — Badaru
  • Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe
  • Matasa Sun Daka Wawasu Kan Tirelar Kayan Agajin Ramadan Na Seyi Tinubu A Gombe 
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa