Aminiya:
2025-04-16@09:24:15 GMT

’Yan sanda sun ceto mutum 23 da aka sace a Kaduna

Published: 3rd, February 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, tare da Sojoji sun samu nasarar ceto mutum 23 da ’yan bindiga suka sace a wani artabu da aka yi a ƙauyen Doka, da ke Ƙaramar Hukumar Kajuru.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Mansur Hassan, ya fitar, ya bayyana cewa babban jami’in ’Yan Sandan yankin Kajuru ne ya jagoranci samamen.

Arsenal ta yi sukuwar salla a kan Man City da ci 5 Osimhen ya maka ɗan jarida a kotu

Ya ce bayan samun bayanan sirri game da maharan, jami’an tsaro sun kai farmaki inda suka ceto dukkanin mutanen 23, waɗanda mazauna Kauru ne.

A yayin artabun, wasu daga cikin maharan sun mutu, yayin da wasu suka tsere cikin daji da raunukan harbin bindiga.

A cewar sanarwar, an sake haɗa mutanen da iyalansu a Ƙaramar Hukumar Kauru.

An luma ƙara tsaurara matakan tsaro a yankin domin tabbatar da cewa babu wata fargaba.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kaduna, Rabiu Muhammad, ya bayyana gamsuwarsa da wannan gagarumar nasarar.

Ya ce za su ci gaba da yaƙi da ta’addanci a Jihar Kaduna bisa jagorancin Gwamnan Jihar, Uba Sani.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Artabu

এছাড়াও পড়ুন:

NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna

 

Kungiyar Kwararrun Masu Fasahar Injiniya ta Ƙasa (NATE) ta rantsar da sabbin shugabannin reshen Jihar Kaduna da za su jagoranci harkokin kungiyar a jihar.

 

Mataimakin Shugaban Yankin Arewa maso Yamma na NATE, Injiniya Bala Muhammad, yayin bikin rantsarwa da aka gudanar a Kaduna, ya bukaci sabbin shugabannin da su fifita haɗin kai da ci gaban ƙungiyar.

 

Sabbin shugabannin da aka rantsar sun hada da: Injiniya Audu John a matsayin Shugaba, AbdulKadir Julde a matsayin Mataimakin Shugaba, sannan Williams Okonkwu a matsayin Sakataren reshen.

 

Sauran su ne Sim Marca Maikege a matsayin Ma’ajin Kuɗi, AbdulGaniu Isah a matsayin Sakataren Kuɗi, da Racheal Ovbiagele a matsayin Sakataren Fasaha.

 

Haka kuma, Engr. Ishaya Buba daga Radio Nigeria Kaduna ya zama Jami’in Hulɗa da Jama’a, Khadijah Abdullahi a matsayin Ko’odinetan Mata, sannan Aliyu Ibrahim Usman a matsayin Sakataren Membobinsu.

 

Matsayin Mai Bincike (Auditor) da Mataimakin Sakatari suna nan a buɗe, ba a cike su ba tukuna.

 

A jawabinsa na kama aiki, sabon Shugaban, Injiniya Audu John, ya jaddada muhimmancin jajircewar mambobi, musamman ta fuskar biyan kuɗin zama dan kungiya da kuma kuden cigaba da zama dan kungiya wato (check-off dues).

Ya ce babu wata ƙungiya da za ta samu ci gaba idan ba tare da sadaukarwar mambobinta ba, kuma za su baiwa wannan bangare muhimmanci sosai.

 

Injiniya Audu John ya kuma bayyana shirin hadin gwiwa da manyan abokan hulɗa, musamman a sashen masana’antu, gwamnati da masu zaman kansu, domin tabbatar da cewa mambobin kungiyar sun samu wakilci da tallafi yadda ya kamata.

 

A cewarsa, shugabannin da suka gabata sun fara irin wannan aiki ta hanyar kai ziyarar girmamawa zuwa kamfanonin Nocaco Nigeria Limited da Hukumar Albarkatun Ruwa domin tantance mambobi da kuma farfado da hulɗar hadin gwiwa.

 

Shugaba Audu ya yaba wa Kwamitin Zaɓe karkashin jagorancin Engr. Silas Oluyori bisa gudanar da zaɓe mai tsafta, adalci da gaskiya duk da kalubalen da suka fuskanta.

 

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Yanki Arewa maso Yamma, Injiniya Bala Muhammad, wanda Jami’in ƙasa na NATE, Injiniya Lukman Sani ya wakilta, ya bayyana cewa reshen Kaduna ne tushen dukkanin rassan NATE a yankin Arewa maso Yamma, amma har yanzu yana fama da kalubale.

 

Ya bukaci sabbin shugabannin su yi aiki tare da juna don dawo da karfin da kuzarin reshen Kaduna kamar yadda aka san shi a da.

 

Ya taya kwamitin zaɓe murna bisa gudanar da zaɓen cikin nasara, tare da tabbatar da ci gaba da tallafa musu don cigaban reshen jihar.

 

Tun da farko a jawabin sa, Shugaban Kwamitin Zaɓe, Engr. Silas Oluyori, ya gode wa duk masu ruwa da tsaki a kungiyar bisa goyon bayan da suka bayar, wanda ya taimaka sosai wajen shawo kan matsalolin da suka fuskanta a lokacin shirya zaɓen.

 

A zantawa da manema labarai, sabon Jami’in Hulɗa da Jama’a, Engr. Ishaya Buba, na gidan Radio Nigeria Kaduna ya bayyana cewa sabbin shugabannin za su kawo sauyi mai amfani wanda zai ɗaga darajar ƙungiyar zuwa mataki mafi girma.

Ya ce, cancanta da jajircewar sabbin shugabannin na nuna alamar cewa za su taka rawa ta kwarai wajen jagoranci da kawo ci gaba mai ma’ana ga reshen Kaduna.

 

REL: Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza
  • Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar
  • Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato
  • Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura
  • Gwamnatin Kebbi Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai A Saudiyya
  • Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna
  • Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno