NAJERIYA A YAU: Dalilin Da Za Mu Kashe Biliyan N2.5 Kan Auren Zawarawa —Gwamnatin Kano
Published: 3rd, February 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Tun bayan da Gwamnatin Kano ta sanar cewa ta ware Naira biliyan biyu da rabi don aura da ’yan mata da zawarawa a jihar batun ke ta shan suka daga ɓangarori daba-daban.
Wasu na ganin jihar na da wasu buƙatun da suka fi auren gatan muhimmanci da ya kamata gwamnatin ta fi mayar da hankali a kansu.
Shirin Najeriya A Yau na wannan rana ya yi nazari ne kan dalilan da Gwamnatin Kano ta ware Naira biliyan biyu da rabi don aurar da ’yan mata da zawarawa.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan mata Hukumar Hisbah
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
Tsohon Shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo ya ce mulkin dimokuraɗiyya ya gaza wajen kawo ci gaba a nahiyar Afirka.
Ya ce tsarin ya gaza ne saboda abin da ya ƙunsa bai zo daidai da al’adu, da yadda ake tafiyar da rayuwa a nahiyar ba, da abubuwan da mutanen nahiyar suka yi amanna da su ba.
Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren GwamnatiTsohon shugaban na wannan furuci ne a Abuja a wurin wani taron bikin cika shekaru 60 a duniya na tsohon mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai kuma tsohon Gwamnan Imo, Emeka Ihedioha.
Obasanjo ya buga misali da yadda tsohon shugaban Amurka, Abraham Lincoln, ya bayyana tsarin dimokuraɗiyya da cewa gwamnati ce ta mutane da mutane ke jagoranta domin al’umma.
Ya ƙara da cewa tsari ne da ake yu domin kowa ya amfana, ba wai wani ɓangaren na al’umma ba ko wasu mutane ƙalilan ba.
Obasanjo ya kuma bayyana cewa kafin zuwan dimokuraɗiyyar ƙasashen yamma, Afirka na da nata tsarin shugabancin wanda ke kula da buƙatun kowa.
A cewarsa wannan tsarin shi ne dimokuraɗiyya, ba abin da ake kira dimokuraɗiyya ba a yau wanda ke bai wa shugabanni damar karɓar duk abin da suke so ba bisa ƙa’ida ba da kuma ta hanyar cin hanci da rashawa su ce wa mutane su je kotu idan suna da ja.
Obasanjo ya ce matuƙar ba a sake fasalin dimokuraɗiyya ta yi daidai da al’adu da manufofin ’yan Afirka da kuma mutunta buƙatun jama’a ba, to za ta ci gaba da durƙushewa kuma a ƙarshe ta mutu murus a nahiyar.
Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar da tsoffin gwamnonin Anambra da Ribas —Peter Obi da Rotimi Amaechi.
Sauran mahalartan sun haɗa da tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo, tsoffin Shugabannin Majalisar Dattawa — David Mark da Ken Nnamani da tsoffin gwamnonin Sakkwato da Kuros Riba — Aminu Waziri Tambuwal da Donald Duke.