Nigeria: “Yan Sanda A Jihar Kaduna Sun Kwato Mutane 23 Daga Hannun Barayin Daji
Published: 3rd, February 2025 GMT
Hukumar ‘yan sanda ta jihar Kaduna ta sanar da cewa ta kwato mutane 23 da masu garkuwa da mutane su ka kama a cikin dajin Kajuru da ke karamar hukumar Kajuru.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar ‘yan sandan jihar Kaduna, Mansir Hassan ya sanar a jiya Lahadi cewa sun kwato mutanan ne a ranar 2 ga watan Febrairu, 2025.
Jami’in ‘yan sandan ya ce sun sami nasarar kwato mutanan ne bayan da su ka sami bayanai na sirri akan kai da komowar masu garkuwa da mutanen.
Haka nan kuma Hassan ya ce, an yi taho mu gama ne da masu garkuwa da mutanen a kusa da kauyen Doka dake karamar hukumar ta Kajuru.
Barayin suna kokarin sauya wa mutanen da su ka yi garkuwa da su, wuri ne a lokacin da ‘yan sandan su ka rutsa da su.
A yayin bata-kashin jami’an tsaro da su ka kunshi ‘yan sanda da kuma sojoji sun kashe barayin masu yawa da kuma tilastawa wadanda su ka saura a raye, janyewa cikin daji.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
Sai dai duk da yaba wa Amurka bisa irin taimakon da ta bayar a baya, Byanyima ta nuna damuwa kan yadda aka dakatar da tallafin kwatsam ba tare da shiri ba.
Wannan na iya haddasa koma baya a ƙoƙarin da aka shafe shekaru ana yi na rage yawan masu kamuwa da cutar, musamman a yankunan da ke fama da talauci da ƙarancin kayan kiwon lafiya.
Masana kiwon lafiya sun bayyana cewa, idan ba a samu sabbin hanyoyin tallafi ba, yiwuwar ƙaruwar mace-mace sakamakon cutar HIV na da matuƙar girma.
Hakan na iya rusa nasarorin da aka samu a yaƙin da duniya ke yi da cutar.
Ana ci gaba da kira ga ƙasashen duniya da ƙungiyoyin agaji da su ceto shirin da ke kare miliyoyin rayuka daga barazanar cutar HIV.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp