Aminiya:
2025-03-25@17:31:00 GMT

Zazzabin Lassa ya kashe mutum biyu a Filato

Published: 3rd, February 2025 GMT

Mutum biyu sun rasu sakamakon bullar cutar zazzabin Lassa a Jihar Filato.

Kwamishinan Lafiya na Jihar Filato, Dakta Cletus Shurkuk, ya sanar cewa mutum na uku da ya kamu da cutar yana samun kulawa a asibiti.

Ya bayyana cewa mamatan sun kamu da cutar ne a Karamar Hukumar Kanam, na ukun da ke raye kuma a Karamar Hukumar Shendam.

Daya daga cikin majinyatan ya rasu ne a Shendam na biyun kuma a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi.

Gwamnatin Najeriya za ta sake ƙara kuɗin lantarki NAJERIYA A YAU: Dalilin Da Za Mu Kashe Biliyan N2.5 Kan Auren Zawarawa —Gwamnatin Kano

Kwamishinan ya bayyana cewa gwamanatin jihar tana aiki tare da Cibiyar Yaki da Yaduwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) domin dakile yaduwar cutar.

Ya ce tun da suka samu rahoton bullar cutar suka tura jami’ansu zuwa yankunan domin yin gwaji ga wadanda suka yi mu’amala da marasa lafiyan da kuma wayar da kan jama’a kan hanyoyin kariyar cutar.

Ya shawarci al’ummar jihar da su kasance masu kula da tsaftar muhalli domin dakile yaduwar cutar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗansanda Ya Kashe Matar Abokin Aikinsa, Ya Jikata Wasu Biyu A Ribas

Wani Sufeto Dansandan da ke aiki a Jihar Kuros Ribas, ya harbe matar abokin aikinsa har lahira tare da jikkata wasu mutane biyu a harbe-harben da ya yi a ranar Lahadi.

Mai magana da yawun rundunar, SP Irene Ugbo, ta tabbatar da faruwar lamarin ga Labarai a birnin Kalaba, inda ta bayyana cewa jami’an Dansandan ya nuna halayyar da ba ta dace ba kafin ya fara harbe-harben.

Ba Na Goyon Bayan Dakatar Da Gwamnan Jihar Ribas – Ndume Bututun Iskar Gas Ya Sake Fashewa A Ribas

Ugbo, ta ƙara da cewa jami’in, naaiki ne a Cibiyar ‘Yansanda ta Atakpa, ya dawo daga aikin dare a wani bankin ‘Microfinance’ kafin afkuwar lamarin. Ta kuma bayyana cewa tuni an kama wanda ake zargi, inda su kuma waɗanda suka jikkata ke samun kulawar likitoci a asibiti.

Bincike ya nuna cewa ɗansandan ya fara nuna alamun taɓun hankali tun bayan dawowarsa daga aikin dare, inda ya rufe ƙofar shiga ofishin ‘yansandan tare da hana kowa fita ko shigowa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD
  • Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi
  • Sin Ta Sanar Da Dokar Dakile Takunkuman Kasashen Waje
  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 2 Kan Zargin Kashe Ɗan Achaɓa Da Sace Babur Ɗinsa A Bauchi 
  • Ɗansanda Ya Kashe Matar Abokin Aikinsa, Ya Jikata Wasu Biyu A Ribas
  • Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani