Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-26@07:55:46 GMT

Uwargidan Gwamnan Jigawa Ta

Published: 3rd, February 2025 GMT

Uwargidan Gwamnan Jigawa Ta

Uwargidan Gwamnan Jihar Jigawa, Hajiya Hadiza Umar Namadi ta kaddamar da wani katafaren  wurin shan shayi da taliya na zamani  a karamar hukumar Maigatari ta jihar.

Hajiya Hadiza Namadi ta ce, wurin sayar da shayin da taliyar da aka zamanantar da shi wani yunkuri ne na karamar hukumar ta Maigatari.

 

Ta kara da cewa, an tsara wannan wurin na zamani ne domin samar da yanayi mai kyau da inganci ga mutane, inda za su ci abinci cikin gamsuwa, tare da bunkasa kasuwanci a yankin.

Hajiya Hadiza ta kuma kaddamar wani tallafi ga mata 300 a karamar hukumar Maigatari.

 

An bayar da naira dubu talatin kowannensu, domin bunkasa kananan sana’o’i.

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, a yayin bikin, uwargidan gwamnan, Hajiya Hadiza Umar Namadi ta gabatar da takardun kama aiki na wucin gadi ga malaman makaranta su 173.

A zantawar wakilinmu da wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, sun yabawa shugaban karamar hukumar Maigatari bisa wannan karimcin.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Karamar hukumar Maigatari karamar hukumar Hajiya Hadiza

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas

Wani sabon kazamin harin sojojin Isra’ila ya yi sanadin shahadar mutum 40 cikin sa’o’I 24 da suka gabata ciki har da Salah al-Bardawil, dan majalisar Falasdinu kuma mamba a ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmaya ta Hamas.

A cikin wata sanarwa da ta fitar yau, Hamas ta ce an kai wa Bardawil hari ne a wani hari na ” yahudawan sahyoniya na ha’inci”, a lokacin da yake gudanar da sallar dare a daren 23 ga watan Ramadan.

An kashe shi ne tare da matarsa ​​a wani hari da Isra’ila ta kai ta sama a kan tantinsa da ke yankin al-Mawasi, yammacin birnin Khan Yunis na kudancin Gaza.

Kungiyar ta bayyana Bardawil a matsayin “alama ta siyasa, yada labarai,” da ayyukan bunkasa al’umma da yankin Falastinu.

Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza a ranar 7 ga Oktoba, 2023, amma ta kasa cimma manufofinta duk da kashe Falasdinawa 49,747, galibi mata da kananan yara, tare da jikkata wasu fiye da 113,213 a yankin da aka yi wa kawanya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Hukumar Birnin Istambul Ta Dakatar Da Akram Imamoglu Daga Matsayinsa Na Magajin Garin Birnin
  • Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa
  • Hajiya Safara’u, Mahaifiyar Gwamna Raɗɗa Ta Rasu
  • Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas
  • Mahaifiyar Gwamnan Katsina ta rasu