Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-02-22@06:19:55 GMT

Uwargidan Gwamnan Jigawa Ta

Published: 3rd, February 2025 GMT

Uwargidan Gwamnan Jigawa Ta

Uwargidan Gwamnan Jihar Jigawa, Hajiya Hadiza Umar Namadi ta kaddamar da wani katafaren  wurin shan shayi da taliya na zamani  a karamar hukumar Maigatari ta jihar.

Hajiya Hadiza Namadi ta ce, wurin sayar da shayin da taliyar da aka zamanantar da shi wani yunkuri ne na karamar hukumar ta Maigatari.

 

Ta kara da cewa, an tsara wannan wurin na zamani ne domin samar da yanayi mai kyau da inganci ga mutane, inda za su ci abinci cikin gamsuwa, tare da bunkasa kasuwanci a yankin.

Hajiya Hadiza ta kuma kaddamar wani tallafi ga mata 300 a karamar hukumar Maigatari.

 

An bayar da naira dubu talatin kowannensu, domin bunkasa kananan sana’o’i.

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, a yayin bikin, uwargidan gwamnan, Hajiya Hadiza Umar Namadi ta gabatar da takardun kama aiki na wucin gadi ga malaman makaranta su 173.

A zantawar wakilinmu da wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, sun yabawa shugaban karamar hukumar Maigatari bisa wannan karimcin.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Karamar hukumar Maigatari karamar hukumar Hajiya Hadiza

এছাড়াও পড়ুন:

IRGC Ta Kaddamar Da Sabbin Makamai A Atisayen Da Take Yi A Halin Yanzu

Dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran ( IRGC) ta yaye kallabin sabbin makamai a atisayen soja mai yaken “Rasulul-A’azam” da suke ci gaba da yi a halin yanzu.

Daga cikin makaman da aka kaddamar da akwai makamai masu linzami dake cin dogon zango, sai kuma jiragen sama marasa matuki da kuma makaman Atilare.

A jiya Laraba ne dai aka kaddamar da sabbin makamai masu linzamin  wanda ya sami halartar manjo janar Muhammad Bakeri da shi ne babban hafasan hafsoshin sojan kasar Iran.

Shi kuwa janar Ali Kuhistani da shi ne mataimakin kwamandan rundunar ta IRGC a fagen kayan yaki, ya ce; Sabbin makamai sun kunshe da kayan aiki na zamani masu muhimmanci da aka hade su wuri daya.

Wannan dais hi ne karo na 19 da IRGC ke gabatar da atisayen mai yaken; Manzon Allah Mafi Girma”.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Dauki Nauyin Dalibai 80 Da Ke Manyan Makarantu
  • Turji Ya Ƙaƙaba Wa Ƙauyen Mataimakin Gwamnan Sokoto Da Wasu Biyan Harajin Miliyan 22
  • Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna Adeleke
  • Gwamnatin Filato ta dakatar da haƙar ma’adinai saboda matsalar tsaro
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • Iran Ta Yi Tir Da Shugaban Hukumar IAEA Saboda Sanya Siyasa Da Daukan Bangare A Jawansa Na Baya Bayan Nan
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa
  • Jakadan Sin Dake Najeriya Ya Gana Da Karamar Ministar Harkokin Wajen Kasar
  • IRGC Ta Kaddamar Da Sabbin Makamai A Atisayen Da Take Yi A Halin Yanzu
  • Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi