Rikicin rusau ya yi ajalin mutum 4 a Kano
Published: 3rd, February 2025 GMT
Aƙalla wasu mutum huɗu sun riga mu gidan gaskiya sakamakon ƙazamin rikicin da ya hautsinen tsakanin mahukunta da mazauna unguwar Rimin Auzinawa da ke Karamar Hukumar Ungogo a Jihar Kano.
Bayanai sun ce an harbe mutanen huɗu ne yayin da suka fito tirjiya kan rusau ɗin gine-gine da jami’an hukumar tsara birane ta Jihar Kano KNUPDA suka aiwatar.
Majiyoyi sun shaida wa Aminiya cewa galibin gidajen da rusau ɗin ya shafa tuni KNUPDA ta shafa musu alamar cewa aiki zai biyo ta kansu.
Ana dai zargin cewa gine-ginen aƙalla 40 da mahukuntan suka rushe an yi su ne a kan fulotan Jami’ar Bayero da ke Kano.
Sai dai wani mazaunin yankin da ya zanta da Aminiya, ya ce tun da jimawa Hukumar ta KNUPDA ta warware wannan matsala kuma ta jaddada musu cewa a halastaccen matsuguninsu suke domin bai shiga harabar jami’ar ba.
“Mun jima da warware wannan matsala da KNUPDA. Sun tabbatar mana cewa gine-ginenmu ba su shiga harabar jami’ar ta Bayero ba.
“Amma kwatsam sai ranar Lahadi da daddare jami’an KNUPDA suka zo suka yi mana rusau.
“A yayin da wasu daga cikin mazauna suka yi ƙoƙarin tirjiya ne suka harbi mutum huɗu da yanzu an yi musu jana’iza. Wannan abun takaici ne.
Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin Manajan Darekta na KNUPDA amma lamarin ya ci tura.
Kazalika, wakilinmu da ya ziyarci ofishin KNUPDA ya tarar da shi fayau a yayin da duk manyan jami’an sun ƙauracewa ofishin domin fargabar kawo musu harin ramuwa kamar yadda wani ƙaramin ma’aikaci ya tabbatar.
“Ana cikin wani yanayi na fargaba a ofishin nan. Shi ya sa ko wurin ajiyar motoci ya zama fayau don duk manyan ma’aikatan babu wanda ya shigo.
“Yanzu haka ƙananan ma’aikata ne kawai suke zaman dabaro a ofishin ba tare da sanin madafar da za a kama ba.
Wani babban Darektan KNUPDA da Aminiya ta tuntuɓa, ya ce ba ma’aikatansu ne suka yi rusau a unguwar ba, inda ya ba da tabbacin cewa jami’ai ne daga Ma’aikatar Ƙasa da Tsara Birane ne suka aiwatar da aikin.
Haka kuma, wani jami’i daga ma’aikatar wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce wuraren da aka yi rusau mallakin Jami’ar Bayero ne kuma nan gaba kaɗan za a fitar da sanarwa a hukumance.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jami ar Bayero Jihar Kano Rimin Auzinawa
এছাড়াও পড়ুন:
An cafke mutum 19 bayan arangama tsakanin sojoji da ’yan shi’a a Abuja
Aƙalla mutum 19 aka kama bayan wata arangama tsakanin mabiya ɗarikar shi’a da jami’an tsaro a Abuja.
Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a a yankin Banex, da ke Wuse 2, inda mutane da dama sun jikkata, sannan mutum ɗaya ya rasu.
An sake harbe wani ƙasurgumin ɗan bindiga a Zamfara Yadda kisan ’yan Arewa 16 a Edo ya tayar da ƙura a faɗin NijeriyaRundunar ’Yan Sandan Birnin Tarayya, ta ce ’yan shi’a sun kai wa jami’an tsaro hari da bindigogi, duwatsu, da wasu makamai.
A sakamakon haka, aka tura ƙarin dakaru domin kwantar da tarzomar.
“Kwamishinan ’yan sanda, CP Ajao Saka Adewale, ya yi tir da wannan hari da aka kai wa jami’an tsaro,” in ji kakakin rundunar, Josephine Adeh.
“Ana ci gaba da bincike, kuma duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.”
Wani ganau da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya bayyana yadda rikicin ya ɓarke.
“Ina wucewa kawai sai naga taron jama’a suna jifan jami’an tsaro. Ba zato ba tsammani, sai aka fara jin harbin bindiga, mutane suka fara gudu,” in ji shi.
Jami’an tsaro sun tabbatar da dawowar zaman lafiya a yankin, sannan sun buƙaci jama’a su zauna lafiya tare da bayar da rahoton duk wank abun zargi.