A kwanan nan, kasar Amurka ta sanar da sanya karin harajin kwastam da ya kai kaso 10% kan kayayyakin da kasar Sin ke fitar da su zuwa kasuwannin Amurka. Wannan mataki ya keta ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya WTO, wanda kuma zai lalata huldar dake tsakanin Sin da Amurka a fannin cinikayya. Yanzu haka, kasar Sin ta ce za ta kai kara ga kungiyar WTO, gami da daukar matakan da suka wajaba wajen kare moriyarta.

A ganin kwararru masu nazarin al’amuran duniya, dalilin da ya sa sabuwar gwamnatin kasar Amurka daukar matakin nan na sanya karin haraji shi ne domin neman tilastawa sauran kasashe su biya kudi, ta yadda kasar Amurka za ta samu damar sassanta matsalar tattalin arziki da take fuskanta. Sai dai an ce matakin zai sa jama’ar kasar Amurka kashe karin kudi wajen sayen kayayyakin masarufi, da rasa dimbin guraben aikin yi.

A nata bangare, matakin da Amurka ta dauka zai sa yawan harajin kwastam da ake kakabawa kayayyakin da kasar Sin ke fitar da su zuwa Amurka kaiwa kimanin kaso 30. Amma hakan ba zai yi tasiri sosai kan tattalin arzikin kasar Sin ba, saboda tun tuni kasar ta fara daidaita manufar fitar da kayayyakinta. Yanzu haka, yawan kayayyakin da Sin take fitarwa zuwa Amurka ya riga ya ragu zuwa kasa da kaso 15%, cikin dukkan kayayyakin da Sin ke fitar da su kasuwannin ketare.

Ban da haka, matakin da kasar Amurka ta dauka na sanya karin harajin kwastam bai shafi Sin kawai ba, wanda shi ma ya jibanci kasashen Mexico da Canada, wadanda suka tabbatar da cewa za su sanya karin haraji kan kayayyakin kasar Amurka don mayar da martani ga matakin Amurka. (Bello Wang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Amurka sanya karin

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta sake kai hare-hare Yemen

Rahotanni daga Yemen na cewa sojojin Amurka sun kai hari a filin tashi da saukar jiragen sama na Hudayda a wani sabon hari kan kasar Yemen tun bayan da Washington ta sanar da kai munanan hare-hare kan kasar dake adawa da hare-haren da Isra’ila ke kai wa al’ummar Gaza.

Tashar talabijin ta al-Masirah ta kasar Yemen ta ce an kai hare-hare ta sama har sau uku a filin jirgin saman da ke gabar tekun Bahar Maliya a daren Asabar.

Kafafan yada labaran Yaman sun kuma bayar da rahoton cewa, an kai hari da jiragen yakin Amurka a tashar jiragen ruwa ta Salif da ke lardin Hudaidah.

Jiragen yakin Amurka sun kara kai hare-hare biyar a gundumar Majzar da ke lardin Ma’rib da ke tsakiyar kasar Yemen.

A wani labarin kuma a lardin Sa’ada dake arewa maso yammacin kasar, sojojin Amurka sun kaddamar da hare-hare ta sama a yankunan Sahar da Kitaf wa al-Boqe’e.

A ranar 15 ga watan Maris ma Amurka ta sanar da kai wani hari ta sama wanda jami’an Yemen suka ce ya kashe mutane 53.

Hare-haren, wanda shi ne na farko tun bayan da Shugaba Donald Trump ya koma kan karagar mulki, ya zo ne bayan da sojojin Yaman suka yi alkawarin sabunta ayyukansu na hana duk wata safarar jiragen ruwa na Isra’ila ko kuma wadanda ke da alaka da Tel Aviv, domin nuna goyan baya  ga al’ummar Falasdinu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sanata Steve Daines
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  • Amurka ta sake kai hare-hare Yemen
  • Karin Sinawa Suna Son Kashe Kudi
  • Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99
  • Sin Za Ta Kara Daidaita Matakan Jawo Jarin Waje
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gargadi Gwamnatin Tarayya Kan Samar Da Karin Jami’o’i
  • Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas