Aminiya:
2025-04-14@17:25:48 GMT

Ya je Maiduguri daga Legas a kan keke

Published: 3rd, February 2025 GMT

Wani mahayin keken hawa, Samuel Fastuma, ɗan asalin Jihar Benue, ya kammala balaguronsa a kan keken hawa daga Legas zuwa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno a cikin kwanaki 8 kacal.

A cewar Fastuma, ya fara wannan tafiya ce a ranar Lahadi 19 ga watan Janairu, 2025 bisa ƙudirinsa na nuna fatan alheri ga daukacin masu yaƙi da fatara da masu yaƙi da muggan ƙwayoyi da kuma neman hadtin kai da zaman lafiya a tsakanin al’ummar Nijeriya.

Rikicin rusau ya yi ajalin mutum 4 a Kano Alawar yara mai sanya maye ta shiga gari —NDLEA

Da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan isar sa birnin na Maiduguri, Fastuma ya ce, ya fara wannan tafiya ce domin yi wa matasa fatan alheri da kuma yin kira da a zauna lafiya a tsakanin ’yan Nijeriya.

Fastuma ya ce, “ina so in sanar da matasa, cewa abubuwa za su daidaita a cikin kasar nan don haka a cigaba da sa rai a kan hakan.

“Na yi imani cewa, idan kuna da basira, ya kamata ku yi amfani da ita domin hakan kan iya haifar da abubuwa masu girma na ci gaba.

“Tafiyar da na yi ta tsawon kwana takwas, na hadu da kalubale da dama da suka hada da rashin kyawun hanyoyin mota a wasu yankunan.”

Fastuma ya ce, “akwai wasu wurare masu kalubale, musamman tsakanin Bida da Npai, inda titin ba shi da kyau sosai.

“Haka nan na kuma fuskanci wasu matsaloli na bin hanyar Kano zuwa Potiskum.”

Duk da wadannan kalubale Fastuma ya jajirce kuma ya samu nasarar isa Maiduguri a ranar 26 ga watan Janairu.

“Na sha jin labarin Jihar Borno, amma wannan shi ne karo na farko da na kawo ziyara,” in ji shi.

‘‘Tsaro a kan titin ya yi matukar tsauri, kuma ya zuwa yanzu, na gano Jihar Borno wuri ne mai dadin rayuwa.”

Tafiya ta ban mamaki irin ta Fastuma tana zama abin sha’awa ga al’umma, musamman lura da halin matsalar tsaro da wasu yankunan kasa ke ciki.

 

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno

Wasu karin majiyoyi sun nuna cewa, wannan hanyar ta hada Maiduguri da wasu kananan hukumomi da ke kudancin jihar Borno, wacce ta kasance yankin da yan ta’addan Boko Haram ke yawan kai hare-hare tsawon shekaru.

 

A baya hanyar, ta kasance a rufe amma Gwamnan jihar, Farfesa Babagana Zulum ya bude ta, domin bai wa jama’a damar ci gaba da zirga-zirga a yankin da suka hada da Damboa, Chibok da sauran kananan hukumomi a kudancin Borno tare da taimakon rakiyar sojoji a matsayin kariya.

 

An kwashe wadanda suka rasun tare da wadanda suka jikkata, wanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba, zuwa asibiti a Maiduguri domin samun kulawar likitoci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno
  • Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
  •  Nigeria: Wani Bom Da Ya Tashi A Maiduguri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 7
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro