Ya je Maiduguri daga Legas a kan keke
Published: 3rd, February 2025 GMT
Wani mahayin keken hawa, Samuel Fastuma, ɗan asalin Jihar Benue, ya kammala balaguronsa a kan keken hawa daga Legas zuwa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno a cikin kwanaki 8 kacal.
A cewar Fastuma, ya fara wannan tafiya ce a ranar Lahadi 19 ga watan Janairu, 2025 bisa ƙudirinsa na nuna fatan alheri ga daukacin masu yaƙi da fatara da masu yaƙi da muggan ƙwayoyi da kuma neman hadtin kai da zaman lafiya a tsakanin al’ummar Nijeriya.
Da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan isar sa birnin na Maiduguri, Fastuma ya ce, ya fara wannan tafiya ce domin yi wa matasa fatan alheri da kuma yin kira da a zauna lafiya a tsakanin ’yan Nijeriya.
Fastuma ya ce, “ina so in sanar da matasa, cewa abubuwa za su daidaita a cikin kasar nan don haka a cigaba da sa rai a kan hakan.
“Na yi imani cewa, idan kuna da basira, ya kamata ku yi amfani da ita domin hakan kan iya haifar da abubuwa masu girma na ci gaba.
“Tafiyar da na yi ta tsawon kwana takwas, na hadu da kalubale da dama da suka hada da rashin kyawun hanyoyin mota a wasu yankunan.”
Fastuma ya ce, “akwai wasu wurare masu kalubale, musamman tsakanin Bida da Npai, inda titin ba shi da kyau sosai.
“Haka nan na kuma fuskanci wasu matsaloli na bin hanyar Kano zuwa Potiskum.”
Duk da wadannan kalubale Fastuma ya jajirce kuma ya samu nasarar isa Maiduguri a ranar 26 ga watan Janairu.
“Na sha jin labarin Jihar Borno, amma wannan shi ne karo na farko da na kawo ziyara,” in ji shi.
‘‘Tsaro a kan titin ya yi matukar tsauri, kuma ya zuwa yanzu, na gano Jihar Borno wuri ne mai dadin rayuwa.”
Tafiya ta ban mamaki irin ta Fastuma tana zama abin sha’awa ga al’umma, musamman lura da halin matsalar tsaro da wasu yankunan kasa ke ciki.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Gombe na ƙarfafa haƙƙoƙin yara masu nakasa — Ƙungiyar JONAPWD
Ƙungiyar Masu Nakasa ta ƙasa reshen Jihar Gombe (JONAPWD), ƙarƙashin jagorancin Shugabanta kuma Sakataren Zartarwa na Hukumar Kula da Masu Nakasa ta Jihar, Dokta Isiyaku Adamu.
Ƙungiyar ta shirya taro na musamman tare da iyayen yara da suke fama da matsala irin ta nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali.
NNPP ta rasa Ɗan Majalisa na farko da ya koma APC Harin ’Yan bindiga: Mun yi asarar shanu sama da miliyan 4 – Miyetti AllahWannan taron na musamman, wanda aka gudanar a ofishin JONAPWD da ke Gombe, ya zama wata muhimmiyar dama don tattauna matsaloli, musayar ƙwarewa da kuma ƙarfafa fafutuka don kare haƙƙoƙin yara masu fama da matsala irin ta nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali.
A jawabinsa, Dokta Adamu ya bayyana cewa yara masu nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali na fuskantar manyan ƙalubale wajen samun ilimi mai inganci, kiwon lafiya mai nagarta da kuma shiga cikin al’umma.
Ya ce, wannan nakasa ta hankali da ta jiki tana nufin yanayi da ke shafar fahimtar ƙwaƙwalwa wajen koyo da hulɗa da jama’a.
Sai dai, Dokta Adamu ya yi nuni da cewa idan aka ba wa waɗannan yara goyon baya mai kyau da fahimta, za su iya bunƙasa basirarsu su yi fice, kuma su bayar da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban al’umma.
Dokta Adamu ya kuma yi bayani ga iyaye game da dokar masu nakasa ta Jihar Gombe da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya rattaba wa hannu kwanan nan. Ya bayyana dokar a matsayin wata gagarumar nasara da za ta tabbatar da kariya, ƙarfafawa da haɗa yara masu nakasa tare da iyalansu cikin al’umma.
Daga cikin muhimman kudurorin taron, akwai ƙarfafa yaƙin wayar da kai don isar da saƙon zuwa ga iyaye da masu kula da yara masu nakasa. Wannan zai taimaka wajen ƙarfafawa al’umma fahimtar baiwa da basirar da yara masu nakasar jiki da kuma ta taɓin hankali ke da ita.
Hakazalika, Dokta Adamu ya nuna godiyarsa ga Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya saboda jajircewarsa wajen inganta rayuwar masu nakasa ta hanyar zartar da dokokin da suka dace.
“Muna matuƙar godiya ga jagorancin gwamna da kuma jajircewarsa wajen tabbatar da rayuwar masu nakasa ta inganta,” in ji shi.