Da Ɗumi-ɗumi: Kotu Ta Dakatar Da Ohinoyi Na Masarautar Ebira
Published: 3rd, February 2025 GMT
Ko da yake har yanzu kotun ba ta bayar da cikakken bayani kan hukuncin ba, amma an gano cewa, shari’ar mai lamba HCO/05C/2024, Dakta Barnabas Adeku Ojiah da wasu mutane biyu ne suka shigar da ita, inda suke kalubalentar hukuncin tsohon gwamnan jihar na Kogi.
Sai dai, jin ta bakin Ohinoyi, Alhaji Ahmed Muhammed Tajani Anaje, ya ci tura yayin da wayoyin sa duk suke kashe a lokacin rubuta wannan rahoto.
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Birnin Istambul Ta Dakatar Da Akram Imamoglu Daga Matsayinsa Na Magajin Garin Birnin
Hukumar birnin istambul ta bada sanarwan dakatar da Akram Imamoglu daga matsayinsa na magajin garin birnin Istambul na wucin gadi, har zuwa lokacinda za’a tabbatar da kubutarsa daga abubuwan da aka zarginsa da su.
Tashar talabijin ta Almayaddeen ta kasar Labanon ta nakalto mahukunta a birnin Istambul na bada labarin cewa za’a zabi wanda zai maye gurbinsa na wucin gadi a ranar Laraba mai zuwa.
Labarin ya kara da cewa ana zirgin Imamoglu da karban rashawa da cin hanci da kuma kafa kungiyar yan ta’adda.
Kama Imamoglu magajin garin na birnin Istambul dai a makon da ya gabata, ya sa dubban daruruwan masu goyon bayansa a birnin Istambul da wasu birane a kasar suka fito kan tituna tare da bukatar a sake shi.
Ana ganin Imamoglu zai iya zaman dan takarar shugaban kasa wanda zai iya kada shugaba Ordugan a zaben shugaban kasa mai zuwa.