Aminiya:
2025-02-22@06:22:18 GMT

Masarautar Fika ta buɗe gasar ƙwallon ƙafa karo na uku a Potiskum

Published: 3rd, February 2025 GMT

Masarautar Fika da ke Jihar Yobe ta buɗe gasar ƙwallon ƙafa karo na uku a filin wasa na Dabo Aliyu da ke garin Potiskum.

An buɗe gasar ƙarƙashin jagorancin mai Martaba Sarkin Fika, Alhaji Dr. Muhammad Ibn Abali Muhammad Idris wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Yobe.

Ya je Maiduguri daga Legas a kan keke Rikicin rusau ya yi ajalin mutum 4 a Kano

Gasar wacce aka fara a shekarar 2011 ta bunƙasa zuwa wani gagarumin taron wasanni a yankin, wadda ke haɗa ƙungiyoyi daga ƙananan hukumomi huɗu na yankin da suka haɗa da Fune, Potiskum, Fika, da Nangere.

A shekarar 2017 aka gudanar da gasar karo  na biyu, lamarin da ya ƙara tabbatar da gasar a matsayin ɗaya daga cikin manyan wasannin ƙwallon kafa a jihar.

A wannan shekarar ta 2025 an buɗe gasar ce da wasa tsakanin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Total Pillars FC Potiskum da Parma FC ita ma a garin na Potiskum.

Ƙungiyoyin biyu dai sun ƙare zagayen farko ba tare da an zura ƙwallo a raga ba, amma ana minti 19 bayan dawowa daga hutun rabin lokaci Abdulzabi na Parma ya zura ƙwallo daya tilo da aka tashi a wasan, inda ƙungiyar tasa ta samu nasara da ci 1-0.

Gasar ta bana ta samu halartar ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa 64 daga ƙananan hukumomi huɗu da suka shiga gasar.

Wani muhimmin abin da ya fi ɗaukar hankali a bikin buɗe gasar shi ne bayar da lambobin yabo ga fitattun mutane domin nuna irin gudunmawar da suke bayarwa wajen wasanni da ci gaban al’ummar wannan masarauta ta Fika.

Waɗanda aka karrama sun haɗa da Alhaji Garba Mohammed, FIFA Lamido, Aliyu Abba Bulama (AFCON), Sadik Rabiu Alkali da Alhaji Ba’aba Abba (Aljino na Fika).

Ana sa ran za a ci gaba da gudanar da gasar nan da makonni masu zuwa, inda za a haɗa haziƙan ’yan ƙwallon ƙafa da masu sha’awar ƙwallon ƙafa daga sassan yankin na Masarautar ta Fika.

Mai Martaba Sarkin Fika, Alhaji Muhammad Ibn Abali Muhammad Idris ya yi fatan alheri ga waɗanda suka samu damar shiga wannan gasa tare da yi musu addu’ar kammala gasar lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Yobe Masarautar Fika ƙwallon ƙafa buɗe gasar

এছাড়াও পড়ুন:

Karyewar Farashi: Ba mu shigo da kayan abinci daga waje ba — Minista

Gwamnatin Tarayya, ta bayyana cewa ba ta shigo da kayan abinci daga ƙasashen waje ba, duk da cewa farashin kayan abinci ya ragu a kasuwanni.

Ministan Aikin Gona da Samar da Abinci, Farfesa Abubakar Kyari, ya bayyana cewa, ko da yake gwamnatin ta yi tunanin shigo da abinci a lokacin da farashinsa ya yi tashin gwauron zabo, daga bisani ta janye wannan shawarar.

An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele Babban mai kai wa Bello Turji makamai ya shiga hannu

Ministan ya danganta saukar farashin kayan abinci da ƙoƙarin manoma da suka koma gonaki a daminar bara, wanda ya sa amfanin gona ya yi yawa.

Ya kuma buƙaci ‘yan kasuwa da su rage farashi domin jama’a su samu sauƙin rayuwa.

Sai dai wasu rahotanni sun bayyana cewa saukar farashin kayan abincin na da alaƙa da wasu dalilai da suka haɗa da shigo da wasu nau’ikan kayan abinci daga waje ba tare da haraji ba.

Wannan mataki da gwamnati ta ɗauka ya taimaka wajen ƙara wadatuwar kayan abinci a kasuwanni, lamarin da ke hana farashinsu tashi.

Har ila yau, ana cikin lokacin girbi, wanda ya sa manoma da yawa suka fito da amfanin gonarsu zuwa kasuwanni.

Yawaitar kayan abinci a hannun ’yan kasuwa ya rage farashin kayayyaki kamar shinkafa, gero, dawa, da wake.

Wani babban dalili da masana tattalin arziƙi suka bayyana shi ne, farfaɗowar darajar Naira a kasuwar musayar kuɗi.

Saukar darajar dala ya sa kayan abinci da ake shigo da su daga waje sun yi sauƙi idan aka kwatanta da watannin baya.

Tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka domin rage tsadar rayuwa, ciki har da sauƙaƙa shigo da abinci, sun taka muhimmiyar rawa wajen rage hauhawar farashi a kasuwanni.

Wannan mataki na ci gaba da samar da sauƙi ga jama’a yayin da ake fatan farashin kayan abinci zai ci gaba da yin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar Wasan Kareti Ta Iran Ta Zama Gwarzo A Asyia
  • Karyewar Farashi: Ba mu shigo da kayan abinci daga waje ba — Minista
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • Ɗaliba ta rasu yayin da gini ya rufta a GGTC Potiskum
  • Yanzu-yanzu: Gini Ya Rufta Wa Ɗaliban GGTC Potiskum
  • Gwamnati Za Ta Haramta Amfani Da Tankoki Masu Ɗaukar Lita 60,000 Aiki Daga Maris 1
  • Real Madrid ta fitar da Man City a Gasar Zakarun Turai
  • Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.
  • Kissoshin Rayuwa. Sirar Imam Alhassan (a) 19
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Mususlunci A Iran IRGC Sun Bada Sanarwan Kai Hari A Kan HKI Karo Na Uku