Aminiya:
2025-02-22@06:37:34 GMT

NCDC ta tsaurara matakan shige da fice a Nijeriya saboda fargabar Ebola

Published: 3rd, February 2025 GMT

Hukumar yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa a Nijeriya (NCDC) ta tsaurara matakan sanya idanu akan hanyoyin shigowa ƙasar sakamakon sabuwar ɓarkewar cutar Ebola a Uganda.

NCDC ta gargaɗi ’yan ƙasar da su guji yin tafiye-tafiye zuwa Uganda saboda ɓullar cutar Ebola da aka tabbatar a ƙasar.

EU ta yaba wa Gwamna Zulum kan farfaɗo da Jihar Borno Masarautar Fika ta buɗe gasar ƙwallon ƙafa karo na uku a Potiskum

Shawarar NCDC na zuwa ne bayan sanarwar Ma’aikatar Lafiya ta Uganda a ranar 30 ga watan Janairun 2025 kan ɓarkewar wani nau’in cutar Ebola mai suna Sudan a gundumomin Wakiso da Mukono da kuma Mbale na ƙasar.

Ko da yake sanarwar NCDC ta ce ba a samu wani rahoto ba game da ɓullar cutar a Nijeriya, sai dai tun da fari dai Hukumar Lafiya ta Uganda ta ce cutar ta yi sanadiyar mutuwar wani mutum ɗaya kana ana kan bincike wasu 44 a ake zargin ya yi mu’amala da su kai-tsaye.

Sakamakon hakan, NCDC a cikin shawarwarin da ta fitar ta ce duk da cewar babu cutar a Nijeriya, amma tana aiki ne domin daƙile shigowarta.

“NCDC tana koƙari wajen sa ido a wuraren shige da fice a Nijeriya tare da sabunta tsare-tsaren bayar da agajin gaggawa da kuma hanyoyin bincike don gano cutar a manyan ɗakunan gwaje-gwaje da ake da su a manyan biranen da ke da filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa,” a cewar sanarwar gargaɗin da NCDC ta fitar wadda ke ɗauke da sa hannu Darakta Janar Jide Idris.

Haka kuma sanarwar ta ce “duk da cewa Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ba ta ayyana dokar hana tafiye-tafiye zuwa Uganda ba, ana gargaɗin duk wanda ya fito daga wuraren da aka samu ɓullar cutar a cikin kwanaki 21 da suka wuce, kuma yake nuna wasu alamomi kamar zazzaɓi da ciwon gabobi da makogwaro da amai da gudawa ko ciwon ciki da dai sauransu, ya gaggauta tuntuɓar Hukumar lafiya ta jihar da yake.”

Kazalika NCDC ta buƙaci ‘yan Nijeriya da su tabbatar an yi musu allurar riga-kafin wasu nau’in cutar Ebola duk kuwa da cewa a yanzu ƙasar ba ta da na nau’in cutar na Sudan da ya ɓarke a Uganda.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iyakokin Nijeriya cutar Ebola

এছাড়াও পড়ুন:

An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai

Hukumomin Jami’ar Tarayya da ke Lokoja a Jihar Kogi, sun rufe jami’ar har zuwa wani lokaci domin daƙile ci gaba da asarar rayuka da dukiya.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun magatakarda kuma sakatariyar majalisar Jami’ar, Dokta Rebecca Aimiohu Okojie, a ranar Alhamis kuma ta bayyanawa manema labarai a Lokoja.

Jihar Gombe na ƙarfafa haƙƙoƙin yara masu nakasa — Ƙungiyar JONAPWD NNPP ta rasa Ɗan Majalisa na farko da ya koma APC

Hukumar Jami’ar ta yi zargin cewa, ɗaliban sun tare babbar ƙofar shiga jami’ar ne tun bayan haɗarin da ya yi sanadin mutuwar ɗaliban jami’ar biyar a ranar Litinin, wanda ya sa shiga harabar jami’ar ke da wuya.

“Rufewar jami’ar ya biyo bayan asarar rayuka da ɗalibai biyar suka yi a wani mummunan haɗarin tirela a Felele, ranar Litinin 17 ga Fabrairu, 2025.

“Tun faruwar lamarin, ɗalibai sun tare ƙofar jami’ar duk da kakkausar murya daga gwamnatin jihar da kuma ƙoƙarin da hukumomin jami’ar suka yi na a kwantar da hankula.

“Saboda haka, bisa shawarar hukumomin tsaro na jihar da kuma daƙile ci gaba da asarar rayuka da dukiya, shugaban jami’ar bayan shawarwarin hukumar ta yanke, shawarar a madadin majalisar jami’ar cewa jami’ar, jami’ar da rassanta za a rufe su har sai baba-ta-gani. Ɗalibai za su bar wuraren karatu kafin ƙarfe 12 na rana ranar Alhamis, 20 ga Fabrairu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Filato ta dakatar da haƙar ma’adinai saboda matsalar tsaro
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • Iran Ta Yi Tir Da Shugaban Hukumar IAEA Saboda Sanya Siyasa Da Daukan Bangare A Jawansa Na Baya Bayan Nan
  • Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah
  • An Haramta Wa Tankokin Man fetur Da Ke Jigilar Lita 60,000 Zirga-zirga A Faɗin Titunan Nijeriya 
  • An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai
  • Wang Yi Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Uganda
  • Kamfanonin Sin Masu Zaman Kansu Na Taka Rawar Gani Ga Bunkasuwar Tattalin Arzikin Duniya
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Gwamnatin Niger Ta Hana Yan Najeriya Dauke Da Passpor Ta Na ECOWAS Shiga Kasar