Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Cewa: Makamai Masu Linzaminsu Zasu Kai Duk Inda Makiya Suke
Published: 3rd, February 2025 GMT
Babban kwamnandan dakarun kare juyin juya halin Musuluncin na Iran ya jaddada cewa: Makamai masu linzamin Iran za su iya kai hari kan kowane makiyi
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Manjo Janar Husaini Salami ya tabbatar da cewa: Makamai masu linzami na Iran suna da karfin kai hari kan duk wani wuri da ke da alaka da makiya a yankin da kuma fatattakar makamai masu linzami, yana mai jaddada cewa; sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci suna da karfin kalubalantar makiya a kowane lokaci.
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musuluncin ya gabatar da jawabi ne a wajen bikin “Malik Ashtar” karo na 14 a safiyar yau Litinin, inda ya ce an kafa dakarun kare juyin juya halin Musulunci ne a matsayin wata mu’ujiza ta ilimi da ta samu kwarin gwiwar abubuwan da suka faru a farkon nasarar juyin juya halin Musulunci na farko, albarkacin wannan rana bisa hangen nesa na marigayi Imam Khumaini {yardan Allah ta tabata a gare shi}.
Ya kara da cewa mayakan da ke kan iyaka suna wakiltar ginshikan tsaro da martabar kasar. Yana mai bayyana cewa: Idan kasar Iran ta samu jin dadin zaman lafiya a cikin tekun wuta, hakan na faruwa ne sakamakon sadaukarwar da wadannan mayaka suka yi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin juya halin Musulunci
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Daraktan Hukumar IAEA, Zai Ziyarci Iran ranar Laraba
Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya zai ziyarci Tehran a ranar Laraba mai zuwa.
Ziyarar ta Grossi na zuwa ne gabanin sabuwar tattaunawar da za’ayi tsakanin Iran da Amurka a ranar Asabar mai zuwa kan batun shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin kasa da kasa Kazem Gharibabadi ya ce shugaban hukumar ta IAEA Rafael Grossi zai ziyarci Tehran a ranar Laraba.
Gharibabadi ya bayyana cewa, babban daraktan hukumar ta IAEA, zai gana da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) Mohammad Eslami.
Ya kara da cewa “ziyarar na cikin tsarin ci gaba da hulda da hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu.”
Ziyarar ta shugaban hukumar ta IAEA za ta zo ne a daidai lokacin da Iran da Amurka ke shirin gudanar da tattaunawar ta biyu, wanda Oman ta shiga tsakani a ranar Asabar data gabata.