Wasannin Lokacin Sanyi Na Asiya Na Harbin Zai Habaka Wasannin Lokacin Sanyi A Asiya
Published: 3rd, February 2025 GMT
A yayin da aka bude wasannin lokacin sanyin na Asiya karo na 9 a birnin Harbin na arewacin kasar Sin a ranar Litinin ta hanyar gabatar da tseren kunna fitila, mai dauke da fitilar, kuma mamban kwamitin wasannin Olympics na kasa da kasa (IOC), Yu Zaiqing, ya bayyana cewa, gasar za ta sa kaimi ga kara yawan wasannin lokacin sanyi a nahiyar Asiya.
Yu ya kara da cewa, tseren fitilar na dauke da ruhin Olympics, wanda ke sanya karin mutane samun zurfin fahimtar wasannin, yana mai cewa, wannan shi ne karo na biyu da Harbin ya karbi bakuncin wasannin lokacin sanyi na Asiya, bayan na karo na 3 da ya gudana a shekarar 1996. Ana matukar sa ran samun ingantattun wuraren gudanar da wasannin da ma mafi kyawun wasannin daga masu wasannin motsa jiki.
Wasannin lokacin sanyi na Asiya na Harbin na 2025 shi ne cikakkun wasannin motsa jiki na lokacin sanyi na kasa da kasa da aka gudanar a kasar Sin a baya-bayan nan, tun bayan gasar Olympics ta lokacin sanyi ta 2022 ta Beijing. (Mai fassara : Mohammed Yahaya)
কীওয়ার্ড: wasannin lokacin sanyi
এছাড়াও পড়ুন:
Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai
Newcastle ta lallasa Leicester da ci 3-0 a ranar Litinin a gasar Firimiya Lig ta Kasar Ingila, wasan wanda ya kasance na 8 a jere da Leicester City ta buga ba tareda jefa kwallo a raga ba, Newcastle da Eddie Howe ke jagoranta na fatan ganin sun samu gurbi a gasar Zakarun Turai na badi, tun da farko dai sun lashe gasar League Cup a watan da ya gabata.
Yanzu haka su na matsayi na biyar a kan teburin Firimiya, inda suke da maki daya da Chelsea da ta ke matsayi na hudu, Leicester City kuma a nata bangaren ka iya komawa gasar ‘yan dagaji ta Championship idan aka doke su a wasansu na gaba a gasar.
Yadda Tashar Jirgen Ruwan Apapa-Moniya Za Ta Taimaka Wa Masu Safarar Fitar Da Kaya NIMASA Za Ta Adana Wa Nijeriya Dala Biliyan 400 A Shekara Daga Cazar Kudaden Safarar KayaNewcastle, wacce arzikinta ya bunkasa tun bayan da mamallakanta ‘yan Kasar Saudiyya su ka karbi iko a shekarar 2021, ta na neman sake samun damar buga gasar Zakarun Turai tun bayan wanda aka kore ta a shekarar 2023/24 bayan shafe shekaru ashirin.
Howe, wanda ya jagoranci Newcastle lashe babban kofi na farko cikin shekaru 56 a wasan da su ka doke Liverpool a Wembley a watan da ya gabata, ya na da damar kara haskakawa a wannan kakar wasanni ta bana mai dimbin tarihi a wajen Newcastle.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp