Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-14@20:05:13 GMT

Muna Jaje Ga Masautar Zazzau – Manjo Janar Bello

Published: 3rd, February 2025 GMT

Kwamandan makarantar horas da sojoji dake Zaria, Manjo Janar Ahmadu Bello Mohammed ya yi alkawarin inganta dangantakar da ke tsakanin makarantar da majalisar masarautar Zazzau.

Ya bayyana haka ne lokacin da ya kai wa mai martaba Sarkin zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ziyarar ban girma a fadar sa dake Zaria.

Manjo Janar Ahmadu Bello, wanda ya bayyana ziyarar a matsayin wani sabon babi a dangantakar daje tsakanin makarantar horas da kuratan da masarautar ta zazzau ya yi alkawarin bunkasa dangantakar dake tsakanin su,ya kuma bayyana cewa ya kai ziyarar ce domin neman albarka da hadin kan majalisar masarautar ta zazzau.

Kwamandan ya kuma mika ta’aziyar makarantar horas da kuratan sojojin ga masarautar ta zazzau bisa rasuwar daya daga cikin yan majalisar masarautar, Alhaji Rilwanu Yahaya Fate,Sarkin Yaki zazzau da ya rasu kwanan nan.

Da ya ke maida jawabi, mai martaba Sarkin zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya gode wa Kwamandan bisa ziyarar, ya kuma yi alkawarin baiwa makarantar ta Dapo duk goyon baya da hadin kai da suke bukata domin sauke nauyin dake kan su.

Mai martaban ya kara da cewa za a gudanar da tsare-tsaren da suka kamata domin daidaita batutuwan dake masarautar ta zazzau da masarautar horas da kuratan sojojin.

Haliru Hamza

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ta aziya masarautar ta zazzau

এছাড়াও পড়ুন:

Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi

’Yan sanda sun kama wani magidanci bisa zargin ya ɗirka wa ’yar cikinsa mai shekara 17 ciki a yankin Kariya da ke Ƙaramar Hukumar Ganjiwa a Jihar Bauchi.

Kakakin ’yan sandan jihar, Ahmed Wakil ya ce an kama mutumin mai shekaru 50 ne bayan samun ƙara cewa ya yi wa ’yar tasa fyaɗe fiye da sau ɗaya a ɗakinsa.

Wakil ya ce a yayin bincike magidancin ya amsa cewa ya sha zakke wa ’yar tasa a gida, kuma bayan an yi mata gwaji a asibiti aka tabbatar cewa tana ɗauke da ciki wata uku.

Ya ce yarinyar ta shaida wa masu bincike cewa a lokacin da mahaifiyarta ta yi tafiya zuwa garin iyayenta a Ƙaramar Hukumar Ningi da ke jihar ne mahaifin nata ya yi amfani da damar ya riƙa lalata da ita.

An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi  Darasi daga rayuwar Dakta Idris AbdulAzeez Dutsen Tanshi ’Yan bindiga sun harbi alkali da ɗansa, sun sace mutane 13 a Katsina

Bayan dawowar mahaifiyar ce ta lura da alamun juna biyu a tare da ’yar, kuma bayan ta titsiye ta, ta shaida mata cewa mahaifinta ne ya yi mata cikin.

Wakil ya ce rundunar tana ci gaba da gudanar da bincike a kan lamarin, kuma kwamishinan ’yan sandan jihar, Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a gurfanar da wanda ake zargin a kotu da zarar an kammala bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Vietnam
  • Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato
  • An Karrama Shugaban Qausain TV, Kanar Sani Bello Da Lambar Yabo
  • Janar Tsiga, Mahaifiyar Rarara da muhimman mutane da aka sace a Katsina
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 108
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi