Aminiya:
2025-03-26@07:51:14 GMT

HOTUNA: Hatsarin tirela ya yi ajalin mutum 4, shanu 15 da awaki 20 a Neja

Published: 4th, February 2025 GMT

Mutum huɗu sun riga mu gidan gaskiya yayin da wasu 13 suka jikkata a sanadiyyar wani mummunan hatsari da ya auku a hanyar Lapai zuwa Agaie da ke Jihar Neja.

Aminiya ta ruwaito cewa hatsarin ya rutsa da tireloli uku waɗanda suka yi karo da juna ’yar tazarar mitoci ƙalilan zuwa garin Agaie.

Mai gari ya tsere bayan mazauna sun cinna wa gidansa wuta a Kano NCDC ta tsaurara matakan shige da fice a Nijeriya saboda fargabar Ebola

Wani mazaunin yankin, Baba Yakubu ya bayyana cewa ɗaya daga cikin tirelolin da lamarin ya shafa ta ɗauko lodin dabbobi da suka haɗa da shanu da awaki

Shi ma Darekta Janar na Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullah Baba Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya bayyana cewa an miƙa waɗanda hatsarin ya rutsa da su zuwa Babban Asibitin Agaie domin samun kulawa.

Ya alaƙanta faruwar lamarin da saɓa wa ka’idar tuƙi a yayin da ɗaya daga cikin tirelolin ta yi ƙoƙarin ƙetare wadda ke gabanta ba bisa ka’ida ba.

Ya ce hatsarin ya yi ajalin mutum huɗu — biyu da suka mutu nan take, sai kuma wasu biyun da suka ce ga garinku nan bayan an miƙa su asibiti.

Kazalika, ya ce shanu kimanin 15 da fiye da awaki 20 sun mutu a dalikin hatsarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: awaki Hatsari Jihar Neja

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa za a samu mutum 2,000 sabbin kamuwa da cutar SIDA duk rana a faɗin duniya.

MDD ta ce tana wannan gargaɗi ne sakamakon matakin Amurka na katse taimakon agajin ƙasashen duniya ƙarƙashin Hukumar ta USAID.

Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas

MDD ta ce ce tilas ne a maye gurbin taimakon idan ana neman kare duniya daga shiga annobar cutar ta AIDS..

Hukumar ta ce muddun Amurka ba ta dawo da tallafin daƙile cutar ba, kuma ba a samu maye gurbin taimakon na Amurka ba, nan da shekaru huɗu za a samu kimanin mutane miliyan 6.3 sabbin masu kamuwa da cutar ta AIDS ko SIDA, gami da samun ƙarin masu mutuwa daga cutar.

Da take jawabi a Geneva a ranar Litinin, Winnie Byinyama, ta ce za a samu sabbin masu kamuwa da cutar aƙalla guda 2,000 kullum saboda janye tallafin, tana mai cewa tuni dubban likitoci da sauran ma’aikatan jinya sun fara rasa aikinsu.

Sai dai duk da haka ta yaba da gudunmawar Amurka wajen tallafa wa ayyukan kiwon lafiya a duniya a gomman shekaru da suka gabata.

Amma ta ce yadda kwatsam aka dakatar da tallafin ba tare da shiri ba, ya fara kawo tsaiko a ƙoƙarin da ake yi na yaƙi da cutar ta HIV.

Alƙaluman da aka fitar a shekarar 2023 sun nuna cewa kimanin mutum 600,000 suka rasa rayukansu a faɗin duniya sakamakon Cutar ta SIDA.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya
  • Sudan: RSF ta hana kayan agaji a yankunan da ke a karkashin ikonta
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]
  • An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Yari A Libya – Gwamnati
  • Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi
  • Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Fiye Da Dalibai 4,200 Suka Amfana Da Tallafin Ilimi Na Sanata Solomon Adeola