Aminiya:
2025-04-26@00:30:04 GMT

Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano

Published: 4th, February 2025 GMT

Babbar Kotun Jihar Kano ta yanke wa wasu mutum biyar hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda laifin lashe wata dattijuwa mai shekara 67, kan zargin ta da maita.

Kotun ya yanke musu hukuncin kisa ne a ranar Litinin bayan samun su da laifin kiran dattijuwar mai suna Ɗahare Abubakar, mayya sannan suka daɓa mata wuka har lahira.

Mai Shari’a Usman Maido, ya bayyana cewa masu gabatar da ka to sun gabatar da gamsassun hujjoji da suka tabbatar da laifin wadanda aka gurfanar.

Waɗanda kana yanke wa hukuncin kisan su ne Da’luta Ibrahim, Abdulaziz Yahaya, Faisal Yahaya, Ibrahim Abdu da Ayuba Abdulrahman.

Mai gari ya tsere bayan mazauna sun cinna wa gidansa wuta a Kano Rikicin rusau ya yi ajalin mutum 4 a Kano NAJERIYA A YAU: Dalilin Da Za Mu Kashe Biliyan N2.5 Kan Auren Zawarawa —Gwamnatin Kano

Tun da farko, mai gabatar da kara, Lamiɗo Abba-Soronɗinki, ya shaida wa koyon cewa da misalin karfe 8.30 na safiyar ranar 23 ga watan Nuwambar shekarar 2023 ne waɗanda ake tuhumar suka hada baki wajen yin aika-aikan.

Ya ce bayan waɗanda ake tuhumar sun zargi Marigayiya Ɗahare da maita ne suka bi ta gona ɗauke da makamai, suka yi mata kisan gilla,

Ya ce an garzaya da ita zuwa Babban Asibitin Wudil inda likitoci suka tabbatar cewa ran dattijuwar ya yi halinsa.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Daɗin Kowa da ke Ƙaramar Hukumar Wudil.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dattijuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa ta jaddada aniyarta na ci gaba da tattaunawar nukiliyar iran

Kasar faransa ta jaddada anniyar na ci gaba da tattaunawa kan shirin nukiliyar iran.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Faransa ya bayyana a ranar Alhamis cewa, Faransa na ci gaba da jajircewa wajen ganin an warware matsalar nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya, kuma a shirye take ta ci gaba da tattaunawa da Tehran.

A yayin taron manema labarai na mako-mako a birnin Paris, Christophe Lemoine ya jaddada cewa: “Muna ci gaba da jajircewa wajen warware matsalar nukiliyar Iran ta hanyar diflomasiyya, kuma a shirye muke mu ci gaba da tattaunawa da Tehran.”

Wannan bayanin na zuwa ne bayan da ministan harkokin wajen Iran Seyyed Abbas Araghchi ya wallafa a shafinsa na sada zumunta na X cewa, Tehran a shirye ta ke ta ci gaba da tattaunawa da kasashen Turai, inda ya bayyana cewa tattaunawar za ta iya bude wata sabuwar hanya.

Araghchi ya bayyana cewa, bayan shawarwarin baya-bayan nan da aka yi a Moscow da Beijing, a shirye yake ya ziyarci Paris, Berlin da London.

Ya kuma ce tun kafin fara tattaunawar da Amurka, Iran na shirye, amma kasashen Turan uku da batun ya shafa ba su nuna sha’awarsu ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya
  • An kama mutum 2 ɗauke da ƙwayar tramadol ta N150m a Kano
  • An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi
  • Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP
  • Faransa ta jaddada aniyarta na ci gaba da tattaunawar nukiliyar iran
  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
  • Congo Da M23 Sun Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
  • Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa
  • Ƙasurgumin Ɗan Fashin Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Mutu Bayan Arangama Da ‘Yansanda A Kano
  • Yawan Falasdinawan Da Suka Yi Shahada Sakamakon Hare-Haren ‘Yan Sahayoniyya Sun Kai 51,266