Aminiya:
2025-04-14@20:35:25 GMT

Kotu ta tsige Ohinoyi na Ƙasar Ebira

Published: 4th, February 2025 GMT

Babbar Kotun Jihar Kogi ta tsige Alhaji Ahmed Muhammed Tajani Anaje daga kujerarsa ta Ohinoyi na Ƙasar Ebira.

Kotun ta soke naɗin Alhaji Ahmed Muhammed ne a ranar Litinin, shekara guda bayan fara aikin basaraken.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a Salisu Umar, ya kuma dakatar da basaraken daga gabatar da kansa matsayin Ohinoyi, har zuwa lokacin da kotun za ta yanke hukuncin ƙarshe.

Kotun ta bayar da umarnin ne bayan ƙarar da Dakta Barnabas Adeku Ojiah da wasu mutum biyu suka shigar.

Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano Mai gari ya tsere bayan mazauna sun cinna wa gidansa wuta a Kano NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba

Sun shigar da ƙara ne suna ƙalubalantar naɗin da Gwamnan Jihar Kogi ya yi wa Alhaji Ahmed Muhammed Tajani Anaje a matsayin Ohinoyi na Ƙasar Ebira.

A watan Disamban 2023 ne tsohon Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello ne ya naɗa Alhaji Ahmed Tijani Anaje a matsayin Ohinoyi na Ƙasar Ebira a yayin da tsohon gwamnan ke shirin sauka daga mulki.

A ranar 8 ga watan Janairun 2024 ne dakataccen sarkin ya fara aiki.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja

A ranar Juma’a da daddare, wata fashewar bama-bama a wata shahararriyar kasuwa a titin Kodesoh, Ikeja dake Lagos ta janyo raunuka ga mutane da dama. Shaidu sun bayyana cewa fashewar ta faru ne lokacin da wani mai kula da shagon kyamara ya yi kokarin bude wani kunshin da aka kawo.

Hukumar agajin gaggawa, tare da jami’an ‘yansanda daga tashar yankin G, EOD-CBRN Base 23 ta Ikeja, da ma’aikatan hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa na jihar Lagos (LASTMA), sun tura jami’ansu domin gudanar da ayyukan daukar matakai da tsaro a wurin.

Kwalara Ta Kashe Mutane 5 A Lagos, An Kai 60 Asibiti Ranga-Ranga Ƴan Nijeriya 85 Za Su Iso Lagos Daga Amurka A Yau

Wani shaida gani da ido, Lucky Okoro, ya bayyana yadda ya samu damar gudu wa daga wurin fashewar, yana mai cewa, “kawai nayi ƙoƙarin shiga shagon, sai fashewar ta afku. Ban jima ba, sai na ga wutar tana kona wani mutum da wata mata a cikin shagon.” Wani shaidar, Olumide Gbeleyi, wanda yake daga wani otel kusa da wurin, ya bayyana cewa, “Mun ji hayaniyar fashewar kuma muka ga hayaki ya rufe ko’ina. Wata mata tana sayar da kayan ciye-ciye a waje ta ji rauni mai tsanani.”

Sule Aminu, wanda ya bayyana yadda abin da ya sani game da lamarin, ya zargi cewa kunshin mai ban mamaki yana dauke da wani abu da aka tura domin cutar da mai shagon.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
  • Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Newcastle Na Gab Da Samun Gurbi A Gasar Zakarun Turai
  • Jama’ar Gabon sun kada kuri’a a zaben shugaban kasa, na farko bayan mulkin zuri’ar Bongo
  • Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi