HKI tana son aiwatar da wani shiri don kara yawan yahudawa a kasar, a dai dai lokacinda take fama da karancin yahudawa a kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta ce a baya dai gwamnatin yahudawan suna son kara yawan  yahudawa musamman a yankin yamma da kogin Jordan, ammam har yanzun shirin baya tafiyar kamar yadda take so.

Labarin ya kara da cewa yawan Palasdinawa a cikin kasar Palasdinu da aka mamaye wata barazana ce babba ga gwamnatin kasar.

Banda haka a cikin yakin watanni 15 da ta fafata da Mutanen yankin Gaza, wasu yahudawa sun fice daga kasar kuma da dama daga cikinsu sun sha alwashin ba za su sake dawowa kasarba. Wasu kuma sun kai ga kona passpot dinsu na HKI tare da nufin ba zasu sake dawowa HKI ba har abada.

Har’ila yau wasu masana sun bayyana cewa duk kokarin da gwamnatin HKI za ta yi na gamsar da yahudawa da ga wasu kasashen duniya dawowa HKI da wuya su sami nasara, musamman ganin a halin yanzu ta shiga cikin yaki wanda ba wanda ya san karshensa ba.

Labarin yace kashi 53% na yahudawan da suke zaune a kasar Falasdinu da aka mamaye sun fito ne daga gabas ta tsakiya da kuma arewacin kasar Amurka. Sanna kashi 36% na yahudawan sahyoniya a HKI sun kaurane daga wasu kasashe.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza

Kafar watsa labaru ta ” Axio ta Amurka ta watsa wani rahoto da yake nuni da cewa, an sami rashin yarda da juna a tsakanin masu zuba hannun jari na kasa da kasa da kuma Amurka.

Kafar watsa labaran ta buga a shafinta na “Internet” cewa; Rashin tabbaci da yake faruwa a halin yanzu a cikin kasuwanni  yana  tsoratar da masu zuba hannun jari a duniya.

Rahoton ya kuma ambaci girgizar da Dalar Amurka take yi, da kuma muhimman takardun da suke a matsayin kaddara a cikin Baitul-malin Amurka.

Kafar watsa labarun ta ce, a baya muhimman takardun da suke a matsayin kaddara a cikin Baitul-malin Amurka, wadanda kuma su ne ke bai wa Dalar Amurka kariya, sun kasance masu karfafa gwiwar masu zuba hannun jari, amma daga makon da ya shude an sami rashin aminci.

Abinda ya faru a makon da ya shude kamar yadda kafar watsa labarun ta ambata yana a matsayin karaurawar hatsari da aka kada, a tsakanin wadanda su ka yi Imani da tsarin kudade da Amurka take jagoranta, tun bayan kawo karshen yakin duniya da biyu.

Haka nan kuma ta yi ishara da cewa a lokacin da aka sami matsalar tattalin arziki a duniya a 2008, da kuma bullar cutar corona a 2020, Dalar Amurka ta rika habaka da tashi sama,amma yanzu akasin haka ne yake faruwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yaya ‘Yan Siyasar Amurka Ke Kasafta Harajin Ramuwar Gayya?
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • Saudiya Tace Shigo Da Agaji Cikin Gaza Bai Da Dangantaka Da Tsagaita Wuta
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Daidaitaccen Tunanin Sin Shi Ne Dabarar Fuskantar Da “Haukar Amurka”
  • Yadda Bankin Stanbic IBTC Ke Bunkasa Tattalin Arzikin Abokan Huldarsa
  • Namibiya ta janye bizar shiga ga wasu manyan kasashe na duniya
  • Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
  • USAID Za Ta Dawo Aiki A Wasu Ƙasashen Duniya – Gwamnatin Amurka