HKI Tana Son Shigo Da Yahudawa Daga Kasashen Duniya Kwararru Da Zasu Bunkasa Tattalin Arzikin Kasar
Published: 4th, February 2025 GMT
HKI tana son aiwatar da wani shiri don kara yawan yahudawa a kasar, a dai dai lokacinda take fama da karancin yahudawa a kasar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta ce a baya dai gwamnatin yahudawan suna son kara yawan yahudawa musamman a yankin yamma da kogin Jordan, ammam har yanzun shirin baya tafiyar kamar yadda take so.
Labarin ya kara da cewa yawan Palasdinawa a cikin kasar Palasdinu da aka mamaye wata barazana ce babba ga gwamnatin kasar.
Banda haka a cikin yakin watanni 15 da ta fafata da Mutanen yankin Gaza, wasu yahudawa sun fice daga kasar kuma da dama daga cikinsu sun sha alwashin ba za su sake dawowa kasarba. Wasu kuma sun kai ga kona passpot dinsu na HKI tare da nufin ba zasu sake dawowa HKI ba har abada.
Har’ila yau wasu masana sun bayyana cewa duk kokarin da gwamnatin HKI za ta yi na gamsar da yahudawa da ga wasu kasashen duniya dawowa HKI da wuya su sami nasara, musamman ganin a halin yanzu ta shiga cikin yaki wanda ba wanda ya san karshensa ba.
Labarin yace kashi 53% na yahudawan da suke zaune a kasar Falasdinu da aka mamaye sun fito ne daga gabas ta tsakiya da kuma arewacin kasar Amurka. Sanna kashi 36% na yahudawan sahyoniya a HKI sun kaurane daga wasu kasashe.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum
Gwamnatin Jihar Borno, ta ɗauki matakin hukunta wasu ma’aurata, Mamman Sheriff da matarsa, da aka kama suna cin zarafin wata yarinya a unguwar Pompomari Bypass da ke Maiduguri.
Bayan bayyanar faifan bidiyon da ya nuna ma’auratan suna dukan yarinyar, mutane da dama sun yi tir da abin a shafukan sada zumunta.
Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar NamibiaWannan ya sa Hukumar Tsaron Sibil Difens (NSCDC) ta cafke su nan take.
Gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum, ya tabbatar da cewa gwamnati ba za ta musu sassauci ba.
Ya ce ma’aikatun shari’a, ilimi, da harkokin mata sun haɗa kai domin ganin an hukunta waɗanda suka aikata laifi.
Yarinyar, wacce ɗaliba ce, ta shiga harabar gidan ma’auratan domin tsinkar mangwaro bayan tashi daga makaranta, inda suka yi mata dukan kawo wuƙa.
A halin yanzu tana kwance a asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), inda Dokta Lawan Bukar Alhaji ya ɗauki nauyin jinyarta.
Gwamnatin Borno ta kuma tallafa wa iyayen yarinyar da kayan agaji, abinci, da kuɗi.
Iyayenta da sauran jama’a sun yaba wa gwamnatin kan matakin da ta ɗauka na kare haƙƙin yarinyar.
Gwamnati ta jaddada cewa duk wanda aka kama da cin zarafin yara ba zai tsira daga hukunci ba.