Tshohon daractan hukumar kare hakkin bil’ada ta MDD Craig Mokhiber ya yi kira ga Amurkawa su dawo daga rakiyar gwamnatin Trump da kuma firai ministan HKI Benyamin Natanyahu, mashayin jinin Falasdiwa, a dai dai lokacinda yake ziyararsa ta farko zuwa kasar Amurka tun bayan da Trump ya sake dawowa fadar White House.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Craig Mokhiber ya na fadar haka a shafinsa na X a jiya litinin, ya kuma kara da cewa, irin tarban da gwamnatin Trump ta bawa Natanyahu, da kuma yadda wasu yan majalisar dokokin kasar suka himmatu, ya nuna cewa babu bambanci a tsakanin gwamnatin Joe Biden da kuma Trump idan an yi maganar dangantar Amurka da HKI.

Yace dukaninsu mashaya jinin Falasdinawa ne, kuma sune suke gudanar da harkokin shugabancin Amurka a bayan fage. Banda haka su ne wadanda suke da biliyoyin dalar Amurka wadanda suke jujjuya duniya da su.  

Yace: Amurka ta kara tallafin da take bawa HKI daga dalar biliyon 03 zuwa dalar biliyon 24 a wannan shekara wanda ya nuna cewa zasu ci gaba da yaki da kuma zubar da jin Larabawa ne fiye da kisan kiyashin da suka yi watani 15 da suka gabata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Ilorin, karkashin jagorancin Mai shari’a Abimbola Awogboro ta yanke wa Musa Buba hukuncin daurin sa’o’i 300 da hidimar al’umma, bisa samunsa da laifin gudanar da harkokin kasuwanci na canji ba tare da wani cikakken lasisi ba.

Hakazalika, alkalin ya kuma yanke hukuncin daure wani Akinwale Olamilekan daga Owena Ijesha a karamar hukumar Oriade ta jihar Osun, daurin sa’o’i 300 (dari uku) da yiwa al’ummar hidima na tsawon sa’o’i biyar a kowace rana ba tare da zabin biyan tara ba, bayan da ya same shi da laifin aikata laifukan da suka shafi yanar gizo wato walawala ko yahoo boyi.

Hukumar dake yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta gurfanar da Musa da Akinwale a gaban kotu a ranar Alhamis, 20 ga Maris, 2025.

Ana tuhumar Musa Buba a wani lokaci a watan Yulin 2024 a kasuwar Chikanda, gundumar Yashikira, a karamar hukumar Baruten, jihar Kwara, yana gudanar da harkokin wata cibiyar hada-hadar kudi, Bureau De Change Business, ba tare da wani sahihin lasisi da babban bankin Najeriya ya bayar ba.

Laifin ya ci karo da Sashe na 57 (1) & (2) na Dokar Bankunan da Sauran Cibiyoyin Kudi, 2020, kuma ana hukunta shi a karkashin sashe na 57(5) (b) na wannan dokar.”

A cikin tuhumar da ake wa Akinwale Olamilekan (Alias: Mary Williams), an zarge shi da samun wani lokaci a watan Nuwamba 2024, da damfara da wata Mary Williams ta hanyar sakon karta kwana na iMessage asusu don karbar kudi $950 (Dalar Amurka Dari Tara da 55) daga wani Mark Durham.

Laifin ya sabawa sashe na 22 (2) (b) (ii) na laifukan Intanet (Hana, Rigakafin, da sauransu) Doka kuma ana hukunta shi a ƙarƙashin sashe na 22 (2) (b) (iv) na wannan Dokar.

Wadanda ake tuhumar sun amsa laifinsu.

 

Da yake tabbatar da gaskiyar lamarin, hujjojin da masu gabatar da kara karkashin jagorancin Andrew Akoja suka gabatar da kuma kararrakin wadanda ake tuhumar, mai shari’a Awogboro ya yanke musu hukunci daidai laifin da suka aikata.

Baya ga hukuncin, kotun ta umurci Musa Buba da ya bata kudaden da suka kai CFA 409,500 da kuma Naira 1,973,200 (Miliyan Daya, Dari Tara da Dubu Saba’in da Uku, Naira Dari Biyu Kadai) ga gwamnatin tarayya.

Hakazalika, Alkalin ya umarci Akinwale da ya ba Gwamnatin Tarayya dalar Amurka $450 (Dalar Amurka dari hudu da hamsin), da kuma wata wayar iphone 12 Pro Max da ya yi amfani da ita wajen aikata laifin.

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An yi wa Jakadan Afirka ta Kudu da Amurka ta kora tarbar Jamurumai bayan komawarsa gida
  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara
  • Araghchi : Ya kamata Duniyar Musulmi ta dauki mataki mai karfi kan Isra’ila
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  •  Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!
  • Za a hukunta ma’auratan da suka ci zarafin yarinya a kan mangwaro — Zulum
  • Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa