Asensio Ya Kammala Komawa Aston Villa Daga PSG
Published: 4th, February 2025 GMT
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Aston Villa ta kammala ɗaukar tsohon ɗan wasan Real Madrid Marco Asensio daga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta PSG a matsayin aro zuwa ƙarshen kakar wasa ta bana.
Asensio wanda ya bar Real Madrid a shekarar 2023 ya na ɗaya daga matasan ƴan wasa da tauraruwarsu ke haskawa a harkar ƙwallon ƙafa a yanzu.
Aston Villa ta wallafa a shafinta na kafar sadarwa cewa Asensio ya rattaɓa hannun komawa ƙungiyar a matsayin aro daga PSG har zuwa ƙarshen kakar wasa ta bana.
Asensio ne ɗan wasa na biyu da Villa ta ɗauka aro bayan Marcus Rashford wanda ta aro daga Manchester United yayin da ake gab da rufe kasuwar saye da sayarwar ƴan ƙwallo a nahiyar Turai.
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
Aƙalla mutum 11 sun shaƙi iskar ’yanci bayan kuɓuta daga hannun ƙungiyar mayaƙan Boko Haram masu iƙirarin jihadi a Jihar Borno.
Waɗanda suka shaƙi iskar ’yancin na daga cikin mutanen da ƙungiyar Boko Haram ta sace a wani wurin kamun kifi a Doron Baga.
Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko HaramWata majiya ta bayyana cewa, wani kwamandan ’yan ta’addan mai suna Tar ne ya jagoranci garkuwa da mutanen ne a ranar 13 ga watan Fabrairu 2025.
Tar da tawagarsa da ke addabar masunta da manoma a gaɓar Tafkin Chadi sun ɗauke mutanen ne yayin da suka afka wa al’ummar Shawaram da ke ƙarƙashin Ƙaramar Hukumar Kukawa ta jihar, inda suka yi awon gaba da mutane 14 da suka haɗa da mata da ƙananan yara.
Wani shugaban al’ummar yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa ’yan ta’addan sun nemi kuɗin fansa jim kaɗan bayan sace su.
Ya bayyana cewa an ceto mutane 11 bayan an biya kuɗin fansa na Naira miliyan 1.4 da wasu al’umma suka tara.
A cewarsa, har yanzu akwai mutane uku da ake garkuwa da su —ciki har da mace guda mahaifinta — a hannun ’yan ta’addan.
Majiyar ta ce mace ta zaɓi ci gaba da zama a hannun ’yan ta’addan saboda sun ƙi sakin mahaifin nata.
Majiyar ta ƙara da cewa Tar ya gindaya sharaɗin cewa muddin ba a biya musu buƙatar sako ragowar mutanen uku ba, zai aurar da macen da ke cikinsu tare da ɗaukar hukunci mai tsanani kan sauran waɗanda ke hannunsa.
Sai dai har zuwa yanzu mahukuntan da wakilinmu ya tuntuɓa ba su ce komai dangane da lamarin ba.