Hukumar ICPC ta samu gurfanar da Mohammed Idris, wani jami’i a ƙofar shigen shiga wurin Hajji da ɗiban kaya na filin jirgin sama na Murtala Mohammed da ke Lagas, kan laifin bayar da bayanan ƙarya da kuma cin da kuɗaɗen haram.

A gaban Mai shari’a O.A. Fadipe na kotun laifuka ta musamman da ke Ikeja, lauyan ICPC, Yvonne Williams-Mbata, ta gabatar da shaida kan yadda bincike ya gano ɓacewar kuɗi har Naira miliyan goma sha ɗaya da dubu ɗari biyu da talatin da huɗu (N11,234,000) a ƙarƙashin kulawar wanda ake tuhuma daga watan Fabrairu 2001 zuwa Afrilu 2021.

Yadda Tayar Jirgin Saman Max Air Ta Kama Da Wuta Yayin Sauka A Kano Fashewar Tayar Jirgi A Kano: Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kamfanin Max Air Na Tsawon Watanni Uku

Mai shari’a Fadipe ta yanke wa wanda ake tuhuma hukuncin ɗaurin shekara guda kan kowanne daga cikin tuhumce-tuhumcen biyu, ko kuma ya biya tarar Naira miliyan ɗaya. Hukuncin zai gudana tare na farko. Haka kuma, an buƙaci ya shiga yarjejeniya da kotu da adadin Naira miliyan biyu (N2,000,000), inda rashin cika sharuɗɗan zai kai shi ga ɗaukar hukuncin ɗaurin shekaru goma.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya sanar da cewa, yara a Gaza suna fuskantar matsakar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba a kan kananan yara.

“Ba mu da wani bayani a tarihin wannan zamani dangane da ke bukatar tallafin lafiyar kwakwalwa kamar yaran Gaza,” in ji mai magana da yawun UNICEF James Elder a wani taron Majalisar Dinkin Duniya a Geneva.

Sannan kuma jami’in  ya yi Allah wadai da tauye hakkin yara da ake yi da gangan a Gaza, ya kuma bukaci masu karfin fada a ji a duniya da su dauki mataki.

Ya kara da cewa an toshe alluran rigakafi 180,000 na rigakafin yara masu mahimmanci, da na’urorin saka jariran da ba su kai ga lokacin haihuwa ba, inda Isra’ila ta hana shigar da wadannan kayayyakia  cikin yankunan zirin gaza.

Babban jami’in na UNICEF ya ce, daukar irin wadannan matakana  kan yara yana a matsayin babban laifi wanda ka iya zama laifin yaki bisa dokoki na kasa d akasa.

A kan haka ya kara jaddada kiransa ga kasashe masu karfin fada a ji da su sauke nauyin da ya rataya a kansu kan batun Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Siyo Man Jiragen Sama Fiye Da Ganga Miliyan 2 Daga Matatar Dangote
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
  • UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara
  • Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno