Aminiya:
2025-03-23@22:03:44 GMT

Yau Majalisar za ta ci gaba da aiki kan Dokar Haraji

Published: 4th, February 2025 GMT

A Talatar nan Majalisar Dokoki ta kasa ta ci gaba zama don hanzarta kammala aiki kan ƙudirin sabuwar dokar haraji mai cike da ruɗani da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar mata.

Bayan zaman farko a ranar 14 da watan nan na Janairu, ta dage zama zuwa ranar 28 domin kwamitoci su kammala aikin tantance kasafin 2025, amma daga bisani ta sake dage zuwa 4 ga Fabrairu domin kwamitocinta su gama sauraron kare kasafin hukumomin gwamnati.

Kafin tafiyar majalisar hutu, an tayar da jijiyoyin a Najeriya kan wasu dokoki hudu na haraji da Shugaba Tinubu ya gabatar wa Majalisar a ranar 13 ga Oktoban 2024.

Gwamnoni da sauran masu ruwa da tsaki na yankin Arewa na zargin dokokoin da nufin danniya da neman talauta yankin, inda suka bukaci a soke dokar.

Amma daga bisani bayan zaman da kungiyar gwamnoni ta kasa (NGF) da Kwamitin Shugaban Kasa kan dokar harajin, aka samu daidaito inda masu adawa da ita suka mayar da wukakensu cikin kube.

Daga cikin matsayar da suka cimma akwai rabon kashi 30% na kudaden harajin sayen kayayyaki (VAT) ga jihohin da aka sayi kayan, maimakon 60% da Tinubu ya nema.

Sun kuma amince da raba 50% na VAT daidai a tsakanin duk jihohi, ragowar 20% kuma gwargwadon yawan al’ummar kowace jiha domin tabbatar da adalci.

Bayan nan ne Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya ce za su nemi goyon bayan ’yan majalisar dokoki ta kasa daga jihohinsu domin ganin dokar ta samu shiga.

Wakilinmu ya ruwaito cewa masu ruwa da tsaki, ciki har da wasu gwamnoni sun kasa sun tsare domin ganin yadda za ta kaya a Majalisar Dokoki ta Kasa kan lamarin dokar mai cike da rudani.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Dokar Haraji

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar

Fadar Shugaban Kasar Nijeriya, ta yi watsi da rahoton baya-bayan nan da kwamitin hulda da kasashen wajen Amurka ya fitar, wanda ya kafa hujja da amincewar majalisar dokokin kasar, na zargin kakaba wa wasu kiristoci takunkumi a kasar.

Mai bai wa shugaban kasa shawara a kan harkokin siyasa, Daniel Bwala, ya bayyana rahoton a matsayin wanda ba shi da tushe da makama, yana mai jaddada cewa; tun bayan lokacin da Shugaba Tinubu ya dare kan kujerar mulki a ranar 29 ga Mayun 2023, al’amuran cin zarafi, musamman ta fuskar addini suka yi matukar ja da baya.

Bwala, ya yi wannan furuci ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, wato na D; yana mai jaddada cewa, gwamnatinsu mai ci yanzu; ta himmatu wajen kokarin daidaita addinai a matsayin abu guda.

“Gwamnatin Bola Tinubu, koda-yaushe na kokarin bai wa addinai muhimmanci na musamman. Tun daga ranar 29 ga Mayun 2023, daidai lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya hau kan karagar mulki, ba a taba samun wasu matsaloli na tsananta wa Kiristoci a ko’ina a fadin wannan kasa ba”, kamar yadda ya rubuta.

Ya jaddada cewa, Nijeriya ta kasance kasa mai dauke da addinai daban-daban, sannan a kowane lokaci gwamnati na kokarin samar da zaman lafiya a tsakanin wadannan addinai.

Martanin da Fadar Shugaban Kasar ta mayar, ya biyo bayan nuna damuwa a kan matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta dauka na amincewa da takunkumin da aka kakaba wa Nijeriya, bisa zargin kashe Kiristoci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Kao Kim Hourn: Ba Ta Hanyar ‘Siddabaru’ Kasar Sin Ta Cimma Nasarori A Fannin Ci Gaba Ba Sai Dai Ta Hanyar Aiki Tukuru Kuma Mai Dorewa
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso
  • Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas