Alakarmu da El-Rufai na nan babu matsala —Uba Sani
Published: 4th, February 2025 GMT
Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna, ya ce babu wata matsala tsakaninsa da tsohon uban gidansa kuma magabacinsa Malam Nasir El-Rufai.
Uba sani ya ce babu kamshin gaskiya a maganganun da ke yawa cewa shi da tsohon gwamnan El-Rufai suna zaman doya da manja.
Ya bayyana haka ne a yayin hirar da kafar tala bijin ta TVC ta yi da shi a ranar Litinin, inda ya ce “alakarmu tana nan yadda ta ke, babu wata matsala, kamar yadda ake rade-radi.
Am fara tunanin cewa dangantaka ta yi tsami tsakanin Uba da El-Rufai ne bayan da gwamnati mai cin ya yi zargin Gwamnatin El-Rufai da barin masa bashin biliyoyin Naira da kuma karkatar da wasu kudade.
Yau Majalisar za ta ci gaba da aiki kan Dokar Haraji Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa BaA kwanakin baya Gwamnatin Uba Sani ta sallami wasu mukarraban El-Rufai da ke cikinta, masu rike da mukaman kwamishinoni kan zargin badakala.
Masu sharhi da magoya bayan tsohon gwamnan dai na zargin Gwamnatin Uba Sani da yi wa Nasir El-Rufai da mukarrabansa bi ta-da-kullin siyasa, zargin da ta karyata.
Zargin El-Rufai da karkatar da kudade, ya kai ga Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta kafa kwamitin binciken El-Rufai, wanda ta ce ta same shi da laifin da ake zargin sa, amma tuni ya musanta zargin.
Amma da aka yi wa gwamnan tambaya game da hakan, ya bayyana cewa bangaren majalisa na aiki ne a matsayin mai cin gashin kansa ba a karkashin gwamna ba, kuma suna da ’yancin gudanar da ayyukansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zargi
এছাড়াও পড়ুন:
EFCC ta gaza tabbatar da tuhumar Murja kan zargin wulaƙanta takardar Naira
Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati, ta gaza tabbatar da zargin wulaƙanta takardar Naira da take yi wa fitacciyar ’yar TikTok ɗin nan, Murja Ibrahim Kunya.
A bayan nan ne EFCC ta gurfanar da Murja a gaban kotu kan zargin cewa ta ci karo da wani bidiyonta tana rawa a kan takardun kuɗi har kimanin Naira dubu 400.
A ƙunshin ƙarar da EFCC ta gabatar mai lamba FHC/KN/CS/18/2025 a gaban wata Kotun Tarayya da ke zamanta a Kano, ta ce laifin da take tuhumar Murja tanadi na Kundin Dokokin Babban Bankin Nijeriya CBN wanda ya haramta wulaƙanta takardar Naira ta kowace siga.