Aminiya:
2025-03-26@02:48:39 GMT

Alakarmu da El-Rufai na nan babu matsala —Uba Sani

Published: 4th, February 2025 GMT

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna, ya ce babu wata matsala tsakaninsa da tsohon uban gidansa kuma magabacinsa Malam Nasir El-Rufai.

Uba sani ya ce babu kamshin gaskiya a maganganun da ke yawa cewa shi da tsohon gwamnan El-Rufai suna zaman doya da manja.

Ya bayyana haka ne a yayin hirar da kafar tala bijin ta TVC ta yi da shi a ranar Litinin, inda ya ce “alakarmu tana nan yadda ta ke, babu wata matsala, kamar yadda ake rade-radi.

Am fara tunanin cewa dangantaka ta yi tsami tsakanin Uba da El-Rufai ne bayan da gwamnati mai cin ya yi zargin Gwamnatin El-Rufai da barin masa bashin biliyoyin Naira da kuma karkatar da wasu kudade.

Yau Majalisar za ta ci gaba da aiki kan Dokar Haraji Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba

A kwanakin baya Gwamnatin Uba Sani ta sallami wasu mukarraban El-Rufai da ke cikinta, masu rike da mukaman kwamishinoni kan zargin badakala.

Masu sharhi da magoya bayan tsohon gwamnan dai na zargin Gwamnatin Uba Sani da yi wa Nasir El-Rufai da mukarrabansa bi ta-da-kullin siyasa, zargin da ta karyata.

Zargin El-Rufai da karkatar da kudade, ya kai ga Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta kafa kwamitin binciken El-Rufai, wanda ta ce ta same shi da laifin da ake zargin sa, amma tuni ya musanta zargin.

Amma da aka yi wa gwamnan tambaya game da hakan, ya bayyana cewa bangaren majalisa na aiki ne a matsayin mai cin gashin kansa ba a karkashin gwamna ba, kuma suna da ’yancin gudanar da ayyukansu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: zargi

এছাড়াও পড়ুন:

An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja

Rundunar ‘yan sandan Birnin Tarayya ta ce ta kama damin alburusai 488 da aka ɓoye a jarkar manja a tashar mota.

Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da ke kula da sintiri na musamman a Abuja, DCP Ishaku Sharu, ne ya bayyana hakan lokacin da yake holen wanda ake zargin a ofishin rundunar a ranar Litinin.

Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas

Ya ce rundunar ta samu nasarar kama wanda ake zargin ne bisa tallafin wasu jami’an ƙungiyar masu sufurin motocin haya (NURTW).

Kazalika, ya ce sun kama wanda ake zargin ne ɗan asalin Jihar Katsina, ɗauke da harsashi 488 na bindigogin AK-47 da ya ɓoye a jarkokin manja.

DCP ya ce bayan rutsa shi ne ya bayyana musu cewa wani Yakubu Kacalla ne ɗan garin Funtua da ke Katsinan ya biya shi N100,000 domin karɓo masa kayan daga wajen wani mutum a Jihar Nasarawa.

Yanzu haka dai wanda ake zargin na hannun ‘yan sanda inda suke ci gaba da bincike domin kamo sauran masu hannu a safarar makaman.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Kan Karfafa Rawar Da MDD Ke Takawa A Beijing
  • Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Zargin Kasar Amurkan Dangane Da Kamfanonin Man Fetur Na Kasar Ba Gaskiya Bane
  • Gaskiyar abin da ake faɗa kan ’yan fim — Samira Sani
  • An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja
  •  Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa