Aminiya:
2025-02-22@06:34:22 GMT

Ma’auratan da aurensu ya mutu sau 12 a shekara 43

Published: 4th, February 2025 GMT

Wasu ma’aurata ’yan kasar Australia da suka yi aure kuma suka sake rabuwa da juna har sau 12 a cikin shekaru 43 da suka gabata, a yanzu ana gudanar da bincike a kan zargin zamba tsakaninsu.

’Yan sanda a birnin Vienna na kasar Australia a halin yanzu suna gudanar da bincike a kan wani lamari mai ban mamaki, inda wasu ma’aurata da suka yi aure sannan suka rabu har sau 12 a tsawon shekaru 43, domin yin amfani da wata doka da ta ba su damar karbar makudan kudade.

Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Adamawa Don namen mulki ’yan siyasa ke sukan Tinubu —Gwamnan Kaduna

Ana zargin tsofaffin ma’auratan da laifin kitsa kowace rabuwa ce a takarda don matar ta samu a biya ta kudin sallama Dala 28,300 kwatankwacin Naira miliyan 43 da dubu dari 440 da dari 783, da aka ba ta bayan mutuwar mijinta na farko ta 1981.

Sun yi amfani da wata dokar kasar Australia da ta ba wa matan da ba su da aure damar a biya su kudin sallama matukar ba ta yi aure ba.

A kowace shekara biyu da rabi, za ta karbi fansho sau 2.5 na zaman zawarci na shekara-shekara, don haka duk shekara uku ko fiye da haka ita da mijinta na biyu za su rabu don ta sami kudin, sa’an nan kuma su sake yin wani auren.

Dabarar yaudarar ma’auratan ta bayyana ne a watan Mayun 2022 lokacin da Cibiyar Inshorar Fansho ta ki sake biyan matar da mijinta ya rasu kudin fansho, duk da rabuwarta a karo na 12 da mijinta na biyu.

Wani bincike ya nuna cewa, ma’auratan sun sake rabuwa, sannan suka yi gaggawar sake daura wani auren duk bayan shekaru uku, a daidai lokacin da matar za ta karbi kudin sallamarta.

Wani bincike da Hukumar Binciken Laifuka ta Graz ta gudanar ya nuna cewa, masu rabuwar auren sun kasance tare a gida daya, suna dafa abinci tare, har ma da kwanciya a gado tare.

A cewar makwabtan nasu, wadanda akasarinsu ba su da masaniya kan al’adar aurensu, sun kasance ma’aurata abin koyi kuma ba su taba rabuwa ba.

Halin nasu ya ankarar da hukuma gano cewa, suna amfani da wannan dabara sama da shekara arba’in.

Hukuncin da Kotun Koli ta yanke a ranar 12 ga Maris, 2024 ya bayyana cewa, “auren da ake yawan saki, sannan a sake daura auren a tsakanin ma’auratan cin zarafin doka ne, idan ba a fasa auren ba, kuma aka yi saki ne kawai don a tabbatar da biyan diyyar kudin fansho ga gwauruwar.”

Ma’auratan na fuskantar zargin yin zamba, inda masu gabatar da kara suka yi zargin cewa sun yi almubazzaranci da kudin sallamar da ya kai Dalar Amurka 341,000 kwantankwaci Naira miliyan 516 da dubu dari 761 da dari 483 da 37 a cikin shekara 43 da suka gabata.

Sai dai, hukumomin Australia ba su amince da rabuwar aure na 12 da ma’auratan suka yi ba, don haka ma’auratan za su fuskanci tuhuma tare.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Australia Ma aurata

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa; Yahudawan Sahayoniyya Sun Kasa Murkushe Gwagwarmaya

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila ta fuskanci cewa dole ta mika wuya tare da amincewa da sulhu da ‘yan gwagwarmaya da ta nemi murkushe su

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Yahudawan sahayoniyya ba su cimma ko daya daga cikin munanan manufofinta ba, kuma daga karshe ya zama tilasta su mika wuya tare da amincewa da sulhu da bangarorin da suke son kawar da su.

Babban sakataren kungiyar jihadul-Islami ta Falasdinu Ziyad Nakhalah, da ya ziyarci birnin Tehran a karkashin jagorancin wata tawaga don tuntubar hukumomin kasar Iran ya gana da ministan harkokin wajen kasar Sayyid Abbas Araqchi a yammacin jiya Talata.

Haka nan yayin da yake ishara da halaltacciyar  gwagwarmayar da al’ummar Falastinu suke yi na neman ‘yancin kai daga ‘yan mamayar yahudawan sahayoniyya tsawon shekaru 80 da suka gabata, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya taya al’ummar Falasdinu murnar samun nasara mai dimbin tarihi da suka samu da kuma juriya kan kisan kiyashin da suka fuskanta daga yahudawan sahyoniya a Gaza na tsawon watanni goma sha shida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tara Naira 16 a taron ƙaddamar da littafin IBB
  • MDD Ta CE Sake Tada Komatsar Tattalin Arzikin Kasar Siriya Zau Dauki Shekaru 50 Nan Gaba
  • Nijar: Taron Kasa Ya Bukaci Sojoji Su Yi Mulkin Rikon Kwarya na Shekara 5
  • Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram
  • Jami’an tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a Sakkwato
  • Jami’in tsaron al’umma 6 sun mutu a artabu da ’yan bindiga a Sakkwato
  • Real Madrid ta fitar da Man City a Gasar Zakarun Turai
  • UCL: Real Madrid ta murƙushe Man City da ci 3
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa; Yahudawan Sahayoniyya Sun Kasa Murkushe Gwagwarmaya
  • Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara