Leadership News Hausa:
2025-02-22@06:26:10 GMT

‘Yan Bindiga Sun Harbe Mutum 2, Sun Yi Garkuwa Da Wasu 5 A Kaduna.

Published: 4th, February 2025 GMT

‘Yan Bindiga Sun Harbe Mutum 2, Sun Yi Garkuwa Da Wasu 5 A Kaduna.

Da yake tabbatar da harin, wani mazaunin T/wada Garmadi, Rumaya Kwassam, Mista Joel Ahada, ya yi Allah wadai da wannan danyen aikin, yana mai bayyana hakan a matsayin rashin mutunta hakkin dan Adam da kare lafiyar mazauna karkara.

 

Kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Kaduna, DSP Mansir Hassan, ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Fansho Na FRCN Da NTA Sun Yabawa Gwamnati Bisa Amincewa Da Biyan Harkokinsu

Ma’aikatan Gidan Rediyon Tarayya (FRCN) da na Hukumar Gidan Talabijin ta Najeriya (NTA) da suka yi ritaya, sun bayyana jin dadinsu kan karin haske da Ministar Kudi ta yi game da wadanda za su ci gajiyar Naira Biliyan 758 da aka amince da su don biyansu kudaden fansho da suke bi.

A tsokacin da suka yi game da lamarin a Kaduna, ’yan fanshon sun bayyana cewa, bayanin ya tabbatar da cewa za a raba kudaden ne zuwa sassa biyu na ma’aikatan da suka yi ritaya a karkashin hukumar fansho ta PTAD da kuma shirin bayar da gudunmawar fansho (CPS).

Sun bayyana fatan cewa za a biya kudaden kafin karshen watan da ake ciki, domin baiwa ‘yan fansho damar gudanar da azumin watan Ramadan cikin kwanciyar hankali da walwala.

Tsohon babban jami’in tsaro na NTA, Alhaji Abdullahi Umar, ya yabawa gwamnatin tarayya bisa wannan tabbacin da ta bayar, ya kuma bukaci kungiyoyin ‘yan fansho da su sanya ido sosai kan yadda ake biyan kudaden domin kaucewa duk wata matsala.

Ya kuma yi kira da a saka ‘yan fansho a cikin shirin inshorar lafiya na kasa (NHIS), wanda a baya aka dawo da shi, domin a taimaka musu wajen kula da lafiyarsu.

 

Suleiman Kaura

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ke ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
  • Kallon-Kallo: Ƙungiyar Ƙwadago Da ‘Yan Nijeriya
  • Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
  • ‘Yan Fansho Na FRCN Da NTA Sun Yabawa Gwamnati Bisa Amincewa Da Biyan Harkokinsu
  • ’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa
  • Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
  • Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane