Sin Ta Sanar Da Daukar Matakan Mayar Da Martani A Kan Karin Harajin Amurka
Published: 4th, February 2025 GMT
Sakamakon sanarwar da Amurka ta fitar kwanan baya a kan kara haraji na kashi 10 cikin dari a kan daukacin kayayyakin kasar Sin da ake kaiwa kasar tare da kafa hujja da wasu batutuwa irin su maganin Fentanyl, a yau Talata, ma’aikatar cinikayya da takwararta ta kudi ta kasar Sin sun fitar da wata sanarwa cewa, Sin ta dauki matakan mayar da martani a kan Amurka tare da fara aiwatarwa.
Matakan da suka jibanci lamarin sun hada da cewa, da farko, kasar Sin za ta sanya harajin kashi 10% zuwa 15% kan wasu kayayyakin da ake shigowa da su daga Amurka, daga ranar 10 ga Fabrairu. Sannan na biyu, kasar Sin ta yanke shawarar shigar da rukunin kamfanonin US PVH da Illumina a cikin jerin kamfanonin da ba su da tabbas. Kana na uku, kasar Sin ta shigar da kara kan matakan da Amurka ta dauka na karin haraji a bangaren sasanta rikici na kungiyar kasuwanci ta duniya, watau WTO.
‘Yan Bindiga Sun Harbe Mutum 2, Sun Yi Garkuwa Da Wasu 5 A Kaduna. Dakarun Sojin Sama Na PLA Sun Yi Shawagin Sintiri A Tsibirin HuangyanKazalika, a gefe guda kuma, kasar Sin ta ba da sanarwar hana fitar da kayayyakin da suka shafi sinadaran hada kayayyakin lantarki da karafa na ‘tungsten’, da ‘tellurium’, da ‘bismuth’, da ‘molybdenum’, da kuma ‘indium’.
Bayan haka, duk dai a yau Talatar, hukumar kula da kasuwannin kasar Sin ta bayyana cewa, ta kaddamar da bincike kan kamfanin Google na Amurka, bisa zargin keta dokar hana kane-kane ta kasar. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
কীওয়ার্ড: kasar Sin ta
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
Isra’ila ta ce ta karbe iko da wata muhimmiyar hanya a zirin Gaza a wani mataki da ya yanke gaba daya yankin kudancin Rafah mai yawan jama’a daga sauran yankunan Falasdinawa da aka yiwa kawanya.
A cikin wata sanarwa da Isra’ila ta fitar yau Asabar ta ce dakarunta sun yi wa Rafah kawanya gaba daya tare da samar da “yankin tsaro” a can.
Sanarwar da ministan harkokin soji na gwamnatin Isra’ila Katz ya fitar ta ce sojojin sun karbe ikon “Morag axis, wanda ke ratsa Gaza tsakanin Rafah da Khan Yunis.”
Katz ya kuma yi kira ga Falasdinawa da su fara kaura zuwa yamma, yana mai gargadin cewa nan ba da jimawa ba za a kara kaimi da fadada ayyukan soji zuwa wasu yankuna a cikin mafi yawancin Gaza.
IDF ta ce ta karɓe da abin da ta bayyana da cibiyar tsaronta da ta yi wa laƙabi da ”Lungun Morag”, sunan wani ginin da Isra’ila ta taɓa yi tsakanin biranen biyu.
A yanzu haka sojojin Isra’ila na gina titi a wurin, da nufin samar da wani wuri da Isra’ila ke iko da shi da ya raba Zirin Gaza.
Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da Hamas ke cewa ta aika wakilanta zuwa Masar domin tattaunawa da masu shiga tsakani kan yiwuwar dawo da yarjejeniyar zaman lafiya.