Lebanon Ta Shigar Da Sabon Korafi Kan Isra’ila A Gaban Kwamitin Sulhu Na MDD
Published: 4th, February 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Labanon ta shigar da sabon korafi kan yahudawan sahyuniya gaban kwamitin sulhu na MDD, inda ta yi Allah wadai da hare-haren baya-bayan nan da yahudawan sahyuniya suka kai kan kasar Labanon, da kuma keta hurimun ikon kasar, da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma yau fiye da watanni biyu.
Wannan korafin, wanda aka mika ta hannun wakilcin Dindindin na Labanon a Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, ya jibanci yadda Isra’ila ta ci gaba da keta yarjejeniyar tun daga ranar 27 ga Nuwamba, 2024 ranar da tsagaita bude wuta ta fara aiki har zuwa yau Talata 4 ga Fabrairu.
Lebanon Ta yi Allah wadai da ci gaba da kai hare-hare ta kasa da ta sama da yahudawan sahyoniya suka yi, da barnata gidaje da matsugunan jama’a, da yin garkuwa da ‘yan kasar Lebanon da sojoji, da kuma hare-haren da ake kai wa fararen hula da ke kokarin komawa kauyukansu da ke kan iyakar kasar ta Lebanon.
Kusan ‘yan kasar Lebanon 24 ne suka yi shahada sannan wasu fiye da 124 suka jikkata a cikin wannan lokaci.
Kan ne kasar Lebanon ta yi kira ga kwamitin sulhu na MDD musamman kasashen da suka dauki nauyi da shiga tsakani wajen cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da su dauki kwararan matakai wajen tunkarar wadannan take-take, tare da yin matsin lamba kan Isra’ila ta mutunta dokokin kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Zargin Kasar Amurkan Dangane Da Kamfanonin Man Fetur Na Kasar Ba Gaskiya Bane
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya musanta zargin kasar Amurka na cewa wasu jiragen ruwan JMI suna amfani da tudan kasar Iraqi sun kai kawo a ruwayen yankin.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta fadawa Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran, kan cewa Aragchi yana fadar haka ne a jiya litinin, a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Iraki Fu’ad Hussain.
Kafin haka ministan ya nakalto korafin da jami’an gwamnatin kasar Amurka suka gabatarwa gwamnatin kasar Iraki na cewa jiragen ruwan kasar Iran na amfani da takardun bugi na kasar Iraki don gudanar da harkokinsu a yankin. Aragchi ya musanta hakan ya kuma kara da cewa gwamnatin kasar Amurka tana son raba JMI da dukkan kasashe makobta don cimma manufofinta na maida kasar Iran saniyar ware a duniya.
Ministocin biyu sun tattauna batun abubuwan da suke faruwa a yankin Asiya ta kudu wadanda suka hada da bautun kissan kiyashin da yahudawan sahyoniyya suke yi a kasar Falasdinu da aka mamaye.
A nashi bangaren ministan harkokin wajen kasar Iraqi ya ce kasar Iraki bada cikin kwancen masu gwagwarmaya a yankin. Wannan kamar yadda kowa ya sani bukata ce daga kasar Amurka na gwamnatin kasar Iraki ta fidda kanta daga kawancen gwagwarmaya wanda kasar Iran take jagoranta a yankin.