HausaTv:
2025-02-22@06:32:31 GMT

Lebanon Ta Shigar Da Sabon Korafi Kan Isra’ila A Gaban Kwamitin Sulhu Na MDD

Published: 4th, February 2025 GMT

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Labanon ta shigar da sabon korafi kan yahudawan sahyuniya gaban kwamitin sulhu na MDD, inda ta yi Allah wadai da hare-haren baya-bayan nan da yahudawan sahyuniya suka kai kan kasar Labanon, da kuma keta hurimun ikon kasar, da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma yau fiye da watanni biyu.

Wannan korafin, wanda aka mika ta hannun wakilcin Dindindin na Labanon a Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, ya jibanci yadda Isra’ila ta ci gaba da keta yarjejeniyar tun daga ranar 27 ga Nuwamba, 2024 ranar da tsagaita bude wuta ta fara aiki har zuwa yau Talata 4 ga Fabrairu.

Lebanon Ta yi Allah wadai da ci gaba da kai hare-hare ta kasa da ta sama da yahudawan sahyoniya suka yi, da barnata gidaje da matsugunan jama’a, da yin garkuwa da ‘yan kasar Lebanon da sojoji, da kuma hare-haren da ake kai wa fararen hula da ke kokarin komawa kauyukansu da ke kan iyakar kasar ta Lebanon.

Kusan ‘yan kasar Lebanon 24 ne suka yi shahada sannan wasu fiye da 124 suka jikkata a cikin wannan lokaci.

Kan ne kasar Lebanon ta yi kira ga kwamitin sulhu na MDD musamman kasashen da suka dauki nauyi da shiga tsakani wajen cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da su dauki kwararan matakai wajen tunkarar wadannan take-take, tare da yin matsin lamba kan Isra’ila ta mutunta dokokin kasa da kasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto

Wani rahoto da kwamitin bincike da Gwamnatin Jihar Kano ta kafa kan zanga-zangar yunwa, ya gano cewa mutum 10 sun rasa rayukansu, yayin da wasu mutum bakwai suka samu munanan raunuka.

Rahoton ya kuma bayyana cewa an yi asarar dukiya da ta kai Naira biliyan 11, sakamakon ƙone-ƙone, sace-sace, da lalata kadarorin gwamnati da na ’yan kasuwa a faɗin jihar.

Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram

Da yake jawabi a taron majalisar zartaswar ta jihar karo na 25 a ranar Talata, Gwamnan Jihar, Abba Kabir Yusuf, ya karɓi rahoton daga shugaban hannun kwamitin, Mai shari’a Lawan Wada (ritaya).

Ya tabbatar da cewa za a fitar da takarda a hukumanci don bayyana waɗanda suka ɗauki nauyin tashin hankali yayin zanga-zangar.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bsture Dawaki Tofa ya fitar, zanga-zangar ta yi sanadin rasuwar rayukan mutum 10, yayin da wasu bakwai duka samu munanan raunuka.

Hakazalika ya ce an yi asarar dukiya da ta kai Naira biliyan 11.

“Na gamsu da gaskiya da ƙwarewar mambobin kwamitin. An zaɓe su bisa cancanta, kuma ina da yaƙinin sun yi aikinsu ba tare da son rai ba,” in ji Gwamna Abba.

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ba ta tsoma baki a binciken da ya ɗauki watanni shida ana yi ba, domin bai wa kwamitin damar gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

“Gwamnati za ta ɗauki matakin da ya dace dangane da abubuwan da aka gano a cikin rahoton.

“Wannan zai zama izina ga masu tayar da tarzoma da haddasa ɓarna a jihar,” a cewarsa.

Da yake gabatar da rahoton, Mai shari’a Wada, ya bayyana cewa kwamitin ya ziyarci wuraren da abin ya shafa tare da tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin tattara bayanai kan tasirin zanga-zangar.

“Alƙawarin da gwamnan ya ɗauka na aiwatar da shawarwarin rahoton yana nuna matakin da za a ɗauka don tabbatar da adalci da daidaito a Jihar Kano,” in ji sanarwar.

Gwamna Abba ya yaba wa kwamitin bisa aikin da suka yi, kuma ya buƙace su da su kasance a shirye idan gwamnati ta sake neman su za su yi wani aiki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila-Hamas: Za’ayi Musayar Fursunonin Karshe Karkashin Yarjejeniyar Farko
  • Tawagogi Na Isa Lebanon Domin Halartar Jana’izar Sayyed Hassan Nasrallah
  • DRC : Kwamitin Tsaro Na MDD, Ya Yi Da Goyan Bayan Da Rwanda Ke Bai Wa ‘Yan Tawayen M23
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa
  • Hamas Za Ta Saki Dukkan Fursunonin Isra’ila Da Ke Hannunta
  • Turkiya Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Sulhu Tsakanin Habasha Da Somaliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa; Yahudawan Sahayoniyya Sun Kasa Murkushe Gwagwarmaya
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Watsi Da Karin Shuruddan Gwamnatin ‘Yan Sayoniyya Kan Tsagaita Bude Wuta
  • Rayuka 10 da dukiyar N11bn sun salwanta yayin zanga-zangar tsadar rayuwa a Kano
  • Mutum 10 sun rasu, an lalata dukiyar N11bn yayin zanga-zangar yunwa a Kano — Rahoto