An Bukaci Gwamnoni Su Yi Koyi Da Gwamnatin Neja Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya
Published: 4th, February 2025 GMT
An shawarci gwamnonin jihohin Arewa da su yi koyi da gwamnatin jihar Neja wajen magance matsalolin rikicin makiyaya da manoma a yankin domin samun ci gaba mai dorewa.
Shugaban kungiyar Miyetti Allah ta kasa MACBAN, Dokta Baba Usman Ngelzarman ne ya bayar da wannan shawarar a wajen wani taro na musamman na karramawa tare da tabbatar da lakabin gargajiya ga wasu fitattun Fulani guda biyu a jihar Neja, da aka gudanar a fadar Sarkin Minna.
Dokta Baba Usman Ngelzarman ya bayyana cewa, hanyar da Gwamna Mohammed Umar Bago na Jihar Neja ya bi na samar da sakamako mai kyau, ta yadda za a rage yawan rikicin makiyaya da manoma a jihar abin a yaba ne matuka.
A cewarsa hakan ya sanya bangarorin 2 sun kara fahimta da mutunta juna, wanda ya haifar da karuwar kudaden shiga a jihar da ma Najeriya baki daya.
Mai martaba Sarkin Minna Dr Umar Faruk Bahago, ya jaddada bukatar masu rike da mukaman gargajiya a yankinsa su rika gudanar da ayyukansu bisa tsoron Allah, ta hanyar yin adalci ga kowa, don samun nasara.
A nasa jawabin sabon Jauro Minna kuma Kwamishinan kula da harkokin Makiyaya da kiwo na jihar Neja, Umar Ahmed Rebe ya yi alkawarin kara himma wajen inganta alakar manoma da makiyaya, wadda za ta ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali da walwala domin samun kyakkyawan sakamako.
A nashi jawabin, Wakilin Fulanin Minna, Alhaji Hassan Usman Shiroro, ya yi kira ga Fulanin jihar Neja da su ci gaba da zama lafiya da kowa domin bunkasa ci gaban jihar Neja cikin hanzari, yana mai jaddada cewa zaman lafiya shi ne abin da ake bukata na duk wani ci gaba mai ma’ana.
Daga Aliyu Lawal
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jihar Neja Kungiyar Miyetti Allah
এছাড়াও পড়ুন:
UNICEF Ya Jinjinawa Jihar Jigawa
Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF, ya ce zai ci gaba da tallafa wa jihar Jigawa wajen gina tsarin kiwon lafiya na al’umma.
Shugaban hukumar UNICEF a Najeriya, Dr. Shyam Sharan-Pathak ya bayyana haka a wajen bikin mika aikin ga gwamnatin jihar Jigawa na tsawon shekaru 3 na GAVI, a hukumance a Dutse babban birnin jihar.
A cewarsa, UNICEF za ta ci gaba da tallafa wa jihar don bunkasa muhimman ayyuka daga cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko na PHC, gami da ayyukan rigakafi na yau da kullun.
Dokta Shyam ya ci gaba da bayyana cewa, gagarumin ci gaban da aka samu ta hanyar shirin, shaida ce ta hadin gwiwa da jajircewa ga kowane yaro, matasa da uwa a jihar da ma fadin kasar nan.
Shugaban ma’aikatan ya yaba da gudunmawar sama da naira miliyan 879 a matsayin tallafin hadin gwiwa na shirin fahimtar juna da gwamnatin jihar Jigawa ta yi, wanda hakan ya sa gwamnatin jihar ta ware kashi 15.6% na kasafin jihar ga sashen kiwon lafiya.
Ya ce, UNICEF ta yaba da GAVI, kawancen rigakafin, saboda tallafin da suke bayarwa don haɓaka ayyukan PHC, don inganta ɗaukar rigakafin yau da kullun da kuma isar da ingantaccen shirin kula da lafiya.
A nasa jawabin, gwamna Umar Namadi ya yabawa hukumar UNICEF da abokan hulda, bisa goyon bayan da suka baiwa fannin kiwon lafiya a jihar a tsawon shekarun da suka gabata na aikin.
Namadi, ya yi nuni da cewa, gwamnatin ta fara aikin farfado da fannin lafiya a matakin farko a jihar.
USMAN MZ