Majalisar Zartarwa ta ware naira biliyan 4.8 domin yaƙi da yaɗuwar cutar HIV a Nijeriya.

Wannan na daga cikin matsayar da aka cimma a taron Majalisar Zartarwa da ya gudana a ranar Litinin kamar yadda Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate ya tabbatar.

Ma’auratan da aurensu ya mutu sau 12 a shekara 43 Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Adamawa

Ministan ya ce wannan yana daga cikin manufofin gwamnatin na inganta kiwon lafiya a matakin farko.

A cewarsa, an tsara kashe kuɗaɗen ne a fannin ɗaukar ma’aikatan lafiya da ba su horo domin samun ƙwarewa da kuma tabbatar da an bayar da kulawar da ta dace domin hana yaɗuwar cutar HIV a sassan ƙasar.

A yayin da abokan hulɗa daban-daban daga ƙetare sun taka rawar gani wajen yaƙi fa cutar, Farfesa Pate ya ce za ta ƙara zage damtse wajen ɗaukar matakan ceto rayuwar mutanen da ke ɗauke da cutar ta HIV.

A bayan nan dai an riƙa bayyana damuwa game da sabbin tsare-tsaren da gwamnatin shugaban Amurka, Donald Trump ta ɓullo da su, musamman a fannin bayar da tallafi, inda ake tunanin za su iya shafar tallafi ga yaƙi da cutar HIV a ƙasashe masu tasowa.

Amma a ranar Asabar gwamnatin Amurkan ta sanar da ware sabon ƙunshin tallafin yaƙi da cutar ta HIV.

Alƙalumman da hukumar hana yaɗuwar cutar HIV a Nijeriya ta fitar, sun ce ƙasar ce ta fi kowacce yawan masu cutar a yammacin Afirka, kuma an daɗe ana samun kiraye-kiraye daga faɗin duniya na ganin Najeriya ta zage damtse wajen yaƙi da yaɗuwar cutar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cutar HIV a

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano

Wata gobara da ta tashi cikin dare a garin Satigal da ke Ƙaramar Hukumar Bunkure a Jihar Kano, ta ƙone gidaje da dama, dabbobi, da rumbunan ajiyar hatsi guda shida.

Sai dai kawo yanzu babu labarin rasa rai a gobarar.

Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan Tsaro

A cewar wata sanarwa da Jami’in Yaɗa Labarai na shiyyar Rano, Rabi’u Kura, ya fitar, mazauna yankin sun haɗa kai wajen kashe gobarar da kuma ceton rayuka da dukiyoyi.

Bayan haka, an kai rahoton lamarin ga Sarkin Rano, Dokta Muhammad Isa Umaru, a fadarsa.

Hakimin Satigal, ya jagoranci wasu mazauna yankin zuwa wajen sarkin, inda suka bayyana cewa gobarar ta lalata gidaje guda shida, kaya, hatsi, dabbobi da kuma wasu kayayyakin amfanin yau da kullum da darajarsu ta kai ta miliyoyin Naira.

Rahotanni sun nuna cewa gobarar ta fara ne sakamakon wuta da aka yi amfani da ita wajen dafa abinci, amma aka bar ta ba tare da an kashe ba.

Sarkin ya jajanta wa waɗanda abin ya shafa kuma ya ba su tallafin Naira 200,000 domin rage musu raɗaɗin asarar da suka yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tara Naira 16 a taron ƙaddamar da littafin IBB
  • Kayan Abinci: Gwamnatin Nijeriya Ta Buƙaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashi
  • UNICEF Ya Jinjinawa Jihar Jigawa
  • Shirin Rigakafin Cututtuka Na UNICEF/GAVI Ya Sami Cikakken Hadin Kan Gwamnatin Jihar Jigawa
  • Wang Yi Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Uganda
  • Gwamnatin Kano Ta Amince da  Kashe Naira Biliyan 33.4 Don Ayyukan Ci Gaba
  • Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa; Yahudawan Sahayoniyya Sun Kasa Murkushe Gwagwarmaya
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alhinin Rasuwar Dattijon Kasa, Edwin Clark