Matsalar “Fentanyl” Ba Laifi Ne Da Amurka Za Ta Iya Dora Wa Wasu Ba
Published: 4th, February 2025 GMT
A kwanan baya, kasar Amurka ta kakaba wa kayayyakin kasar Sin da ake neman shigar da su cikin kasuwanninta karin harajin kwastam na kaso 10%, bisa dalilin wai Sin na sayar da magani mai suna Fentanyl a kasar.
Hakika maganar Fentanyl din wani batu ne da kasar Amurka ta dade tana kokarin ruruta shi, inda wasu ‘yan siyasar kasar ke neman dora laifin yadda mutanen kasar ke amfani da maganin a matsayin miyagun kwayoyi kan kasar Sin, cewa wai “Sin na samar da sinadarin hada maganin Fentanyl, wanda aka sarrafa shi zuwa miyagun kwayoyi a Mexico, tare da kai su cikin Amurka”.
Sai dai a ganin Farfesa Li Haidong na jami’ar diflomasiyya ta Sin, gwamnatin Amurka ta yi sakaci wajen sa ido kan yadda ake amfani da maganin Fentanyl a cikin gidanta, abin da ya sa batun ya zama wata matsalar da ake fuskanta a kasar. Sa’an nan, da gwamnatin kasar Amurka ta ga ta kasa magance matsalar daga tushe, sai ta fara dora laifi ga sauran kasashe da suka hada da Sin da Mexico, don nuna wa jama’arta cewa tana daukar mataki. Ban da haka, ta mai da maganar Fentanyl a matsayin wani dalili na daukar matakin karin haraji kan kayayyakin kasar Sin. (Bello Wang)
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno
An kama wani jami’in rundunar sa-kai ta JTF, Modu Mallam Gana mai shekaru 27 a garin Monguno, bisa zarginsa da harbin wasu gungun matasa wanda ya yi sanadin mutuwar mutane biyu tare da raunata daya.
Wata majiyar leƙen asiri ta shaida wa Zagazola Makama cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 6:15 na safiyar ranar 21 ga Maris, 2025, a lokacin da wasu matasa suka tsaya a gaban ofishin dakarun da ke Unguwar Bakin Kasuwa, a Karamar Hukumar Monguno.
Mahaifiyar Gwamnan Katsina ta rasu Yadda ake noman gurjiyaMajiyar ta ce wanda ake zargin Modu Mallam Gana ya harzuka da tsayarwar matasan a bakin ofishinsu, lamarin da ya bude musu wuta.
Wadanda abin ya shafa — Ya’zainab Bum da Goni Mohammed Ahmadu — sun mutu nan take yayin da Hamsatu Ali ta samu munanan raunuka kuma aka kwantar da ita a babban asibitin Monguno.
Sai dai an tabbatar da mutuwar Ya’zainab Bum da Goni Mohammed Ahmadu, inda aka mika wa iyalansu gawarwakinsu domin yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada yayin da Hamsatu Ali tana kwance a asibiti tana jinya.
Majiyar ta ce an kama wanda ake zargin nan take, kuma aka mika shi ga ‘yan sanda don gudanar da binciken da ya dace da shi.