A kwanan baya, kasar Amurka ta kakaba wa kayayyakin kasar Sin da ake neman shigar da su cikin kasuwanninta karin harajin kwastam na kaso 10%, bisa dalilin wai Sin na sayar da magani mai suna Fentanyl a kasar.

Hakika maganar Fentanyl din wani batu ne da kasar Amurka ta dade tana kokarin ruruta shi, inda wasu ‘yan siyasar kasar ke neman dora laifin yadda mutanen kasar ke amfani da maganin a matsayin miyagun kwayoyi kan kasar Sin, cewa wai “Sin na samar da sinadarin hada maganin Fentanyl, wanda aka sarrafa shi zuwa miyagun kwayoyi a Mexico, tare da kai su cikin Amurka”.

Sa’an nan Amurka ta fake da wannan dalili tana kakaba wa kamfanonin Sin takunkumi, har ma ta kaddamar da matakin hukuncin haraji a wannan karo.

Sai dai a ganin Farfesa Li Haidong na jami’ar diflomasiyya ta Sin, gwamnatin Amurka ta yi sakaci wajen sa ido kan yadda ake amfani da maganin Fentanyl a cikin gidanta, abin da ya sa batun ya zama wata matsalar da ake fuskanta a kasar. Sa’an nan, da gwamnatin kasar Amurka ta ga ta kasa magance matsalar daga tushe, sai ta fara dora laifi ga sauran kasashe da suka hada da Sin da Mexico, don nuna wa jama’arta cewa tana daukar mataki. Ban da haka, ta mai da maganar Fentanyl a matsayin wani dalili na daukar matakin karin haraji kan kayayyakin kasar Sin. (Bello Wang)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno

An kama wani jami’in rundunar sa-kai ta JTF, Modu Mallam Gana mai shekaru 27 a garin Monguno, bisa zarginsa da harbin wasu gungun matasa wanda ya yi sanadin mutuwar mutane biyu tare da raunata daya.

Wata majiyar leƙen asiri ta shaida wa Zagazola Makama cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 6:15 na safiyar ranar 21 ga Maris, 2025, a lokacin da wasu matasa suka tsaya a gaban ofishin dakarun da ke Unguwar Bakin Kasuwa, a Karamar Hukumar Monguno.

Mahaifiyar Gwamnan Katsina ta rasu Yadda ake noman gurjiya

Majiyar ta ce wanda ake zargin Modu Mallam Gana ya harzuka da tsayarwar matasan a bakin ofishinsu, lamarin da ya bude musu wuta.

Wadanda abin ya shafa — Ya’zainab Bum da Goni Mohammed Ahmadu — sun mutu nan take yayin da Hamsatu Ali ta samu munanan raunuka kuma aka kwantar da ita a babban asibitin Monguno.

Sai dai an tabbatar da mutuwar Ya’zainab Bum da Goni Mohammed Ahmadu, inda aka mika wa iyalansu gawarwakinsu domin yi musu jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada yayin da Hamsatu Ali tana kwance a asibiti tana jinya.

Majiyar ta ce an kama wanda ake zargin nan take, kuma aka mika shi ga ‘yan sanda don gudanar da binciken da ya dace da shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • ECOWAS Za Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • Rasha ta ce tana nazari kan sakamakon tattaunawar
  •  Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
  • UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
  • Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Sanata Steve Daines
  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Jakadan Sin A Amurka: Mayar Da Karin Haraji Makami Kaikayi Ne Da Zai Koma Kan Mashekiya
  • Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]