Leadership News Hausa:
2025-03-25@19:37:15 GMT

Wakilin Sin: Dakile Ci Gaban Fasahohin Zamani Ba Zai Yi Tasiri Ba

Published: 4th, February 2025 GMT

Wakilin Sin: Dakile Ci Gaban Fasahohin Zamani Ba Zai Yi Tasiri Ba

Babban wakilin kasar Sin a MDD Fu Cong, ya gudanar da taron manema labarai a hedkwatar MDD dake birnin New York, jiya Litinin bisa agogon birnin, domin gabatar da muhimman tsare-tsare na wa’adin shugabancin kasar Sin a kwamitin sulhu, na wannan wata.

A cewar Fu Cong, a yayin wa’adin shugabancin kwamitin sulhu na MDD a watan nan, kasar Sin za ta mai da hankali kan ra’ayoyin bangarori daban-daban da gudanar da tsarin mulkin duniya, da kula da halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya da kuma yanayin da ake ciki a wasu kasashen Afirka.

Da aka tambaye shi game da samfurin kirkirarriyar basira ta DeepSeek, wanda wani kamfanin kula da fasahohin kirkirarriyar basira na kasar Sin ya fitar, Fu Cong ya jaddada cewa, kada a raina hazakar masu binciken kimiyya da fasaha na kasar Sin, domin DeepSeek ya jawo hankulan mutane a duniya, kuma ya sa wasu mutane cikin damuwa da tsoro, wanda ke nuna cewa, dakile fasahohi ba zai yi tasiri ba, kana wannan darasi ne da ya kamata kasashen duniya, musamman ma Amurka, su koya.(Safiyah Ma)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewa za a samu mutum 2,000 sabbin kamuwa da cutar SIDA duk rana a faɗin duniya.

MDD ta ce tana wannan gargaɗi ne sakamakon matakin Amurka na katse taimakon agajin ƙasashen duniya ƙarƙashin Hukumar ta USAID.

Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas

MDD ta ce ce tilas ne a maye gurbin taimakon idan ana neman kare duniya daga shiga annobar cutar ta AIDS..

Hukumar ta ce muddun Amurka ba ta dawo da tallafin daƙile cutar ba, kuma ba a samu maye gurbin taimakon na Amurka ba, nan da shekaru huɗu za a samu kimanin mutane miliyan 6.3 sabbin masu kamuwa da cutar ta AIDS ko SIDA, gami da samun ƙarin masu mutuwa daga cutar.

Da take jawabi a Geneva a ranar Litinin, Winnie Byinyama, ta ce za a samu sabbin masu kamuwa da cutar aƙalla guda 2,000 kullum saboda janye tallafin, tana mai cewa tuni dubban likitoci da sauran ma’aikatan jinya sun fara rasa aikinsu.

Sai dai duk da haka ta yaba da gudunmawar Amurka wajen tallafa wa ayyukan kiwon lafiya a duniya a gomman shekaru da suka gabata.

Amma ta ce yadda kwatsam aka dakatar da tallafin ba tare da shiri ba, ya fara kawo tsaiko a ƙoƙarin da ake yi na yaƙi da cutar ta HIV.

Alƙaluman da aka fitar a shekarar 2023 sun nuna cewa kimanin mutum 600,000 suka rasa rayukansu a faɗin duniya sakamakon Cutar ta SIDA.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD
  • Sin Ta Sanar Da Dokar Dakile Takunkuman Kasashen Waje
  •  Jam’iyyar “Turkish National Party” Ta Tsaid Imam Uglu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa
  •  Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Karfafa Gwiwar Kamfanonin Kasashen Duniya Da Su Fadada Zuba Jari A Sin 
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Game Da Tunanin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam Da Kin Amincewa Da Siyasantar Da Hakkin Dan Adam