Don neman mulki ’yan siyasa ke sukar Tinubu —Gwamnan Kaduna
Published: 4th, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya soki ’yan siyasar da ke sukar gwamnatin Shugaban Bola Tinubu da cewa suna yi ne kawai domin neman mulki.
Uba Sani ya bayyana cewa ’yan siyasar da ke yawan sukan Tinubu a baya-bayan nan ba su da wani abin da za magance matsalolin Najeriyar da suke suka shugaban kasan a kai.
Ya kara da cewa masu sukan Tinubun su ne suke ta yabon shugaban kasar, amma yanzu da mulki ya bar hannunsu suka dawo suna zagin sa.
A cewarsa, babu mutum daya a cikin taron masu kushe Tinubun da ke da nagartar da ta fi shugaban kasar, yana mai jaddada cewa Tinubu ya yi yaki kai da fata kuma har yanzu yana kare muradun tsarin dimokuradiyya.
Alakarmu da El-Rufai na nan babu matsala —Uba Sani Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa BaIdan ba a manta ba a makon jiya ne a yayin wani taro da suka gudanar a Abuja, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar da takwaransa na Jam’iyyar LP, Peter Obi da tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Ribas, Rotimi Amaechi, da tsohon Gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi da sauransu suka salon mulkin Tinubu da jam’iyyar APC.
Amma a yayi wata hira da aka yi da shi a tashar talabijin na TVC a ranar Litinin, Gwamna Uba Sani ya bayyana zargin nasu matsayin mara tushe.
Ya ce, “yawancin wadannan ’yan siyasan kamar a kan kansu suke magana. Ai da a jam’iyya daya muke da su, don haka ina makamin abin da suke yi.”
Ya bayyana maganganun nasu da soki-burutsu da “neman wautar da hankalin ’yan Najeriya,” amma ai yawancinsu masu rike mukaman gwamnati ne kimanin shekaru biyu da suka gabata, mai suka yi a lokacin?”
Don haka ya zarge su da sukan Tinubu domin samun karbuwa a wurin ’yan Najeriya a yunkurinsu na samun madafun iko.
Amma ya ce, “’Yan Najeriya na da hankuale, sun san cewa ’yan siyasar na yakar Tinubu ne kawai saboda babu abin da suka fi shi da shi. Sun samu dama a bayan, amma me suka yi da ita?”
Ya kara da cewa yawancin masu sukar Shugaban Kasar su ke yabon Tinubu, amma da suka sauka daga mulki sai suka sauya baki.উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan Najeriya Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Sanata Katung ya damu kan yadda wasu ta’azzara ta’addanci a kudancin Kaduna
Sanata Sunday Marshall Katung, mai wakiltar Kudancin Kaduna a Majalisar Dattawa, ya bayyana damuwarsa kan yadda wasu mazauna yankin ke taimaka wa miyagu wajen aiwatar da ayyukan ta’addanci.
Da yake magana a taron manema labarai na Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Kudancin Kaduna (SKJF) a Zonkwa, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Zangon Kataf, Sanata Katung, ya jaddada cewa hukumomin tsaro na kara ɗaukar matakan daƙile matsalar a Kauru, Kachia da sauran yankunan da abin ya shafa.
Wasu sassan Abuja za su kasance cikin duhu a ƙarshen mako – TCN Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Peter ObiYa gargaɗi duk masu bai wa ’yan ta’adda mafaka ko goyon baya da su daina, domin hukuma za ta ɗauki matakin ladabtar da su.
Sanatan ya kuma bayyana aniyarsa ta horar da matasa a fannin fasahar zamani da ICT domin su samu ƙwarewa da damar gogayya a matakin ƙasa da ƙasa.
Har ila yau, ya yaba da ƙoƙarin shugabanni da masu ruwa da tsaki wajen samar da Jami’ar Fasaha ta Tarayya da ke Kachia, wacce yanzu ke da reshe a garin Manchok.
Dangane da batun canza Asibitin Tunawa da Sir Patrick Ibrahim Yakowa da ke Kafanchan zuwa Cibiyar Lafiya ta Tarayya, Katung, ya bayyana cewa ƙudirinsa yana jiran sauraron ra’ayoyi a Majalisar Dattawa.
Ya ƙara da cewa ƙudiri makamancinsa a Majalisar Wakilai ya riga ya kai matakin karatu na uku, kuma bayan amincewar Majalisar Dattawa, za a haɗa su don gabatar wa Shugaban Ƙasa domin ya rattaba hannu.
Bugu da ƙari, Sanatan ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da ta bai wa malaman kimiyya fifiko wajen ɗaukar sabbin malamai a makarantun sakandare domin inganta harkar ilimi.
A nasa ɓangaren, Shugaban SKJF, Ango Bally, ya ce taron manema labaran wani ɓangare ne na ƙoƙarin ƙungiyar na wayar da kan jama’a kan ayyukan Sanata Katung a Majalisar Dattawa.