Aminiya:
2025-03-26@06:03:44 GMT

Don neman mulki ’yan siyasa ke sukar Tinubu —Gwamnan Kaduna

Published: 4th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya soki ’yan siyasar da ke sukar gwamnatin Shugaban Bola Tinubu da cewa suna yi ne kawai domin neman mulki.

Uba Sani ya bayyana cewa ’yan siyasar da ke yawan sukan Tinubu a baya-bayan nan ba su da wani abin da za magance matsalolin Najeriyar da suke suka shugaban kasan a kai.

Ya kara da cewa masu sukan Tinubun su ne suke ta yabon shugaban kasar, amma yanzu da mulki ya bar hannunsu suka dawo suna zagin sa.

A cewarsa, babu mutum daya a cikin taron masu kushe Tinubun da ke da nagartar da ta fi shugaban kasar, yana mai jaddada cewa Tinubu ya yi yaki kai da fata kuma har yanzu yana kare muradun tsarin dimokuradiyya.

Alakarmu da El-Rufai na nan babu matsala —Uba Sani Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba

Idan ba a manta ba a makon jiya ne a yayin wani taro da suka gudanar a Abuja, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar da takwaransa na Jam’iyyar LP, Peter Obi da tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Ribas, Rotimi Amaechi, da tsohon Gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi da sauransu suka salon mulkin Tinubu da jam’iyyar APC.

Amma a yayi wata hira da aka yi da shi a tashar talabijin na TVC a ranar Litinin, Gwamna Uba Sani ya bayyana zargin nasu matsayin mara tushe.

Ya ce, “yawancin wadannan ’yan siyasan kamar a kan kansu suke magana. Ai da a jam’iyya daya muke da su, don haka ina makamin abin da suke yi.”

Ya bayyana maganganun nasu da soki-burutsu da “neman wautar da hankalin ’yan Najeriya,” amma ai yawancinsu masu rike mukaman gwamnati ne kimanin shekaru biyu da suka gabata, mai suka yi a lokacin?”

Don haka ya zarge su da sukan Tinubu domin samun karbuwa a wurin ’yan Najeriya a yunkurinsu na samun madafun iko.

Amma ya ce, “’Yan Najeriya na da hankuale, sun san cewa ’yan siyasar na yakar Tinubu ne kawai saboda babu abin da suka fi shi da shi. Sun samu dama a bayan, amma me suka yi da ita?”

Ya kara da cewa yawancin masu sukar Shugaban Kasar su ke yabon Tinubu, amma da suka sauka daga mulki sai suka sauya baki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI

Shugaban majalisar dokokin kasar Lebanon Nabih Berry ya bayyana cewa HKI tanason jawosu cikin tattaunawar diblomasiyya wanda zai kai kasar ga samar da huldar jakadanci da ita, amma mu bama tare da wannan ra’ayin.

Nabih Berry ya bayyana haka ne a lokacinda yake zantawa da jaridar ‘Sharqul Awsad’ ya kuma kara da cewa a halin yanzu muja jiran HKI ta aiwatar da dukkan abubuwan da suka zo cikin yarjeniyar tsagaita wuta ta 1701 wacce kasashen duniya suka amince da ita, amma HKI ta ki aiwatar da ita a yayinda kungiyar Hizbullah ta luzumci tsagaita budewa juna wata na wannan yarjeniyar.

Shugaban majalisar dokokin kasar ta Lebanon ya kara da cewa, a halin yanzu HKI take ficewa daga kasar Lebanon daga wasu wurare kimani biyar wanda hakan ya hana sojojin kasar Lebanon shiga wurare don tabbatar da cewa suna kula da dukkan kan iyakoki na kasar. Banda haka sojojin HKI suna keta hirumin wannan yarjeniyar, wanda yakata a aiwatar da ita watanni 6 da suka gabata. Tana kai hare-hare a kudancin kasar da kuma wasu wurare a Biqaa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • SDP: Ba Mu Yi Wa Kowa Alƙawarin Takarar Shugaban Ƙasa Ba
  •  Jam’iyyar “Turkish National Party” Ta Tsaid Imam Uglu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa
  •  Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas
  • Wasu manyan ’yan Nijeriya sun yi wa Gwamna Radda ta’aziyya a Saudiyya
  • Dole Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Ta Daina Barazana Ga Masu Sukar Ta – Amnesty
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027