Aminiya:
2025-04-16@04:40:36 GMT

Don neman mulki ’yan siyasa ke sukar Tinubu —Gwamnan Kaduna

Published: 4th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya soki ’yan siyasar da ke sukar gwamnatin Shugaban Bola Tinubu da cewa suna yi ne kawai domin neman mulki.

Uba Sani ya bayyana cewa ’yan siyasar da ke yawan sukan Tinubu a baya-bayan nan ba su da wani abin da za magance matsalolin Najeriyar da suke suka shugaban kasan a kai.

Ya kara da cewa masu sukan Tinubun su ne suke ta yabon shugaban kasar, amma yanzu da mulki ya bar hannunsu suka dawo suna zagin sa.

A cewarsa, babu mutum daya a cikin taron masu kushe Tinubun da ke da nagartar da ta fi shugaban kasar, yana mai jaddada cewa Tinubu ya yi yaki kai da fata kuma har yanzu yana kare muradun tsarin dimokuradiyya.

Alakarmu da El-Rufai na nan babu matsala —Uba Sani Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba

Idan ba a manta ba a makon jiya ne a yayin wani taro da suka gudanar a Abuja, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar da takwaransa na Jam’iyyar LP, Peter Obi da tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Ribas, Rotimi Amaechi, da tsohon Gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi da sauransu suka salon mulkin Tinubu da jam’iyyar APC.

Amma a yayi wata hira da aka yi da shi a tashar talabijin na TVC a ranar Litinin, Gwamna Uba Sani ya bayyana zargin nasu matsayin mara tushe.

Ya ce, “yawancin wadannan ’yan siyasan kamar a kan kansu suke magana. Ai da a jam’iyya daya muke da su, don haka ina makamin abin da suke yi.”

Ya bayyana maganganun nasu da soki-burutsu da “neman wautar da hankalin ’yan Najeriya,” amma ai yawancinsu masu rike mukaman gwamnati ne kimanin shekaru biyu da suka gabata, mai suka yi a lokacin?”

Don haka ya zarge su da sukan Tinubu domin samun karbuwa a wurin ’yan Najeriya a yunkurinsu na samun madafun iko.

Amma ya ce, “’Yan Najeriya na da hankuale, sun san cewa ’yan siyasar na yakar Tinubu ne kawai saboda babu abin da suka fi shi da shi. Sun samu dama a bayan, amma me suka yi da ita?”

Ya kara da cewa yawancin masu sukar Shugaban Kasar su ke yabon Tinubu, amma da suka sauka daga mulki sai suka sauya baki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da kudirin kafa sashen kula da masu fama da matsalar kwakwalwa a jihar ya zama doka.

Dokar za ta samar da kariya da kuma bunkasa ‘yancin masu fama da matsalar kwakwalwa musamman masu tu’ammuli da muggan kwayoyi a fadin jihar Kaduna.

Da yake jagorantar zaman majalisar, shugaban majalisar dokokin jihar kaduna, Yusuf Dahiru Liman ya sanar da amincewa da kudirin wanda aka yiwa lakabi da kudirin kula da lafiya masu fama da cutar kwakwalwa na jihar Kaduna.

Da yake gabatar da rahoto, shugaban kwamitin hadin gwiwa na lafiya da sharia, wanda aka dorawa alhakin yin nazari a kan wannan kudiri, Mr. Haruna Barnabas ya ce sun yi nazarin kudirin sannan sun gano cewa akwai bukatar a karfafa matakan da jihar ke bi wajen kula da masu fama da matsalar kwakwalwa domin bunkasa lafiyar kwakwalwa da magance kalubalen da masu tu’ammuli ke fuskanta a cikin al’umma.

Ya ce sabuwar dokar za ta taimaka wajen sauya suna tare da manufofin Hukumar Yaki da Tu’ammuli da Muggan Kwayoyi ta Jihar Kaduna-KADBUSA zuwa Hukumar Yaki da Tu’ammuli da Muggan Kwayoyi da Kula da Lafiyar Kwakwalwa ta Jihar Kaduna-KADSAMHSA domin ya dace da yadda ake tafiyar da irin wadannan ayyuka a matakin duniya.

A cewar shugaban kwamitin, za ta tabbatar da cewa ana mutunta masu tu’ammuli da muggan kwayoyi, da gyara dabi’un su da kuma sake shigar da su cikin al’amuran al’umma don su bada gudunmuwa mai ma’ana.

A wani labarin kuma, majalisar dokokin jihar Kaduna ta mika wani kudiri dake bukatar kafa Hukumar Kula da Ilimin Manyan Makarantun Sakandare, na 2025.

Kudirin, wanda dan majalisa mai wakiltar birnin Zaria a majalisar dokokin jihar Kaduna, Barrister Mahmud Lawal Isma’ila ya ce kudirin zai inganta tsarin ilimin jihar ya dace da ci gaban zamani.

Ya ce idan aka amince da kudirin ya zama doka, hukumar za ta rika kula da dukkanin manyan makarantun sakandare a fadin jihar, don tabbatar da ganin ana sarrafa kudaden da aka ware ma bangaren ilimi don ganin ya habbaka.

Shamsuddeen Mannir Atiku

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza
  • Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar
  • Kasashen Da Mata Ba Su Taba Mulki Ba A Tarihi
  • Yaƙin Neman Zaɓe A 2027: Ƙungiya Ta Nemi A Maye Gurbin Mai Magana Da Yawun Shugaban Ƙasa
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
  • An Karrama Shugaban Qausain TV, Kanar Sani Bello Da Lambar Yabo
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran