Ministan ya kara da cewa, za a kaddamar da kashin farko na gyaran madatsar ruwan a tsakanin watan Fabrairu zuwa Yulin 2025.

 

Ya kuma kara jaddada muhimmancin wannan aiki na tabbatar da cewa ba a samu ambaliyar ruwa a jihar Borno a shekarar 2025 ba.

.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta sake kai hare-hare Yemen

Rahotanni daga Yemen na cewa sojojin Amurka sun kai hari a filin tashi da saukar jiragen sama na Hudayda a wani sabon hari kan kasar Yemen tun bayan da Washington ta sanar da kai munanan hare-hare kan kasar dake adawa da hare-haren da Isra’ila ke kai wa al’ummar Gaza.

Tashar talabijin ta al-Masirah ta kasar Yemen ta ce an kai hare-hare ta sama har sau uku a filin jirgin saman da ke gabar tekun Bahar Maliya a daren Asabar.

Kafafan yada labaran Yaman sun kuma bayar da rahoton cewa, an kai hari da jiragen yakin Amurka a tashar jiragen ruwa ta Salif da ke lardin Hudaidah.

Jiragen yakin Amurka sun kara kai hare-hare biyar a gundumar Majzar da ke lardin Ma’rib da ke tsakiyar kasar Yemen.

A wani labarin kuma a lardin Sa’ada dake arewa maso yammacin kasar, sojojin Amurka sun kaddamar da hare-hare ta sama a yankunan Sahar da Kitaf wa al-Boqe’e.

A ranar 15 ga watan Maris ma Amurka ta sanar da kai wani hari ta sama wanda jami’an Yemen suka ce ya kashe mutane 53.

Hare-haren, wanda shi ne na farko tun bayan da Shugaba Donald Trump ya koma kan karagar mulki, ya zo ne bayan da sojojin Yaman suka yi alkawarin sabunta ayyukansu na hana duk wata safarar jiragen ruwa na Isra’ila ko kuma wadanda ke da alaka da Tel Aviv, domin nuna goyan baya  ga al’ummar Falasdinu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • Bututun Iskar Gas Ya Sake Fashewa A Ribas
  • Yadda garin Zip ya nutse a Kogin Binuwai
  • Amurka ta sake kai hare-hare Yemen
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari
  • Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99
  • Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun
  • Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
  • An kori shugaban hukumar leken asiri ta cikin gidan Isra’ila