Shugaban Majalisar Wakilai Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Shugaban Kamfanin Albabello
Published: 5th, February 2025 GMT
Shugaban Majalisar Wakilai Dr Abbas Tajuddeen, ya bayyana kaduwarsa bisa rasuwar fitaccen dan kasuwa kuma mai taimakon jama’a, Alhaji Bala Abdulwahab da ke Zariya, wanda aka fi sani da Albabello.
A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Malam Musa Abdullahi Krishi ya fitar, Dakta Abbas Tajuddeen, ya ce masarautar Zazzau da jihar Kaduna sun yi rashin babban dan kasuwa wanda ya sadaukar da rayuwarsa gaba daya wajen yi wa al’umma hidima.
Shugaban majalisar ya jaddada cewa, Albabello, ta hanyar sahihancinsa na kasuwanci, ya samar da ayyukan yi ga dubban jama’a a Zariya da ma fadin kasar nan, ta hanyar amfani da rassan kamfaninsa daban-daban.
Ya ci gaba da cewa Albabello, ya kuma gina makarantun firamare da sakandare da dama don inganta ilimi; da masallatai, domin ci gaban al’umma.
Hakazalika, a yayin rayuwarsa marigayin ya dauki nauyin bayar da tallafin karatu ga dalibai don yin karatu a Najeriya da kasashen waje, da sauransu.
Dr Tajuddeen, ya yi addu’a ga Allah SWT dayYa ji kan marigayi Alhaji Bala Abdulwahab, Ya kuma bai wa iyalansa hakurin jure rashin.
Alhaji Bala Abdulwahab, wanda shi ne wanda ya assasa kamfanin Albabello Trading Company Limited da ke Zariya, ya rasu ne a ranar Litinin 3 ga watan Fabrairun 2025, yana da shekaru 68.
Daga Salihu Tsibiri
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Rasuwa Shugaban Majalisar Wakilai
এছাড়াও পড়ুন:
Moscow : Dole ne Rasha da China su shiga tattaunawar nukiliya da Iran
Kasar Rasha ta bayyana cewa dole Moscow da Beijing su shiga shawarwarin tattaunawar nukiliya da Iran.
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta bayyana cewa, Moscow a shirye take ta samar da ingantacciyar hadin gwiwa da dukkan bangarorin kan batun yarjejeniyar nukiliyar Iran. “
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa ya aike da wasika zuwa Tehran domin fara tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran; yayin da shi da kansa ya fice daga yarjejeniyar nukiliyar Iran a wa’adinsa na farko.
A halin da ake ciki dai ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta mayar da martani ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump a cikin kwanaki masu zuwa ta hanyoyin da suka dace.
Araghchi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kai tsaye a gidan talabijin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran (IRIB) ranar Alhamis.
Araghchi ya kuma lura cewa a wannan karon, ci gaban ya zo tare da wani yunkuri na diflomasiyya daga Amurkawa, ciki har da wasika da bukatar yin shawarwari.
Ya kuma bayyana cewa manufar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a bayyane take. “Ba za mu shiga tattaunawa kai tsaye karkashin matsin lamba, barazana, ko karin takunkumi.”
Ministan harkokin wajen kasar ya kuma bayyana cewa wasikar “mafi yawan barazana ce,” amma kuma akwai damamaki a ciki.
A farkon watan Maris ne Trump ya bayyana cewa ya rubuta wasika zuwa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.