Rundunar ‘Yan Sanda a Jihar Kebbi, ta kama wasu bakin haure 165 tare da mika su ga hukumar kula da shige da fice ta kasa shiyar  jihar domin gudanar da bincike.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar ya fitar kuma ya mikawa gidan rediyon Najeriya a jihar Kebbi, ya ce, bisa rahoton bayanan sirri, an gano sama da mutum dari biyu a wani katafaren gida mai dakuna uku da ke unguwar Kuwait a cikin birnin Birnin Kebbi.

Sanarwar ta ce, tawagar jami’an ‘yan sanda da ke sashin binciken manyan laifuka (SCID) ce ta kai samame unguwar, inda suka yi nasarar cafke mutane dari da sittin da biyar (165).

Ya bayyana cewa, yayin da ake gudanar da bincike, an gano cewa, dukkan wadanda ake zargin sun fito ne daga kasashen Faransa da suka hada da Burkina Faso, da  Jamhuriyar Benin, da Jamhuriyar Nijar, da Mali da Ivory Coast.

A cewar sanarwar, bincike ya kara nuna cewa, wadanda ake zargin suna zaune ne a Najeriya ba tare da wasu takardu masu inganci ba.

Sanarwar ta ce, bayan kammala binciken farko da rundunar ta gudanar, an mika wadanda ake zargin  zuwa hukumar kula da shige da fice ta kasa shiyyar jihar Kebbi, domin ci gaba da bincike da kuma daukar matakin da ya dace.

Daga Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hukumar Kula da Shige da Fice

এছাড়াও পড়ুন:

Harin ’Yan bindiga: Mun yi asarar shanu sama da miliyan 4 – Miyetti Allah

Ƙungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah (MACBAN) ta yi iƙirarin cewa wasu ’yan bindiga sun sace sama da shanu miliyan huɗu na mambobinta musamman a yankin Arewa maso Yamma.

Shugaban Ƙungiyar MACBAN na ƙasa, Baba Usman ne ya bayyana hakan a yayin ƙaddamar da sababbin zaɓaɓɓun shugabannin ƙungiyar na jiha a Jihar Kebbi.

’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina

Ya ce, ɓarayin shanu na yawan kai wa Fulani makiyaya hari, lamarin da ke haddasa asarar rayuka da dukiyoyi.

Usman ya jaddada cewa, ana yawan sauya fahimtar Fulani makiyaya da kuma yin kuskuren sanya su a matsayin masu tayar da fitina, inda ya buƙaci jama’a su riƙa ganin su a matsayin ’yan Najeriya masu son zaman lafiya.

Ya kuma yi kira ga makiyaya da su guji shiga gonaki, su kuma zauna lafiya da manoma domin hana rikice-rikice.

Usman ya kuma yabawa gwamnatin tarayya da na jihohi bisa kafa ma’aikatar kiwo, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen magance matsalolin da makiyaya ke fuskanta.

Ya kuma yabawa gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris bisa ayyukan da suka inganta rayuwar al’ummar Fulani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Rangadi A Karamar Hukumar Jahun
  • Shugaba Tinubu Ya Yaba Da Gudunmawar Da IBB Ya Bayar Yayin Mulkinsa
  • Hamas Ta Mika Gawawwakin ‘Yan Isra’ila Hudu Ga Kungiyar Red Cross
  • Harin ’Yan bindiga: Mun yi asarar shanu sama da miliyan 4 – Miyetti Allah
  • Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram
  • NAJERIYA A YAU: Tanadin Dokar Kasa Kan Kirkirar Gwamnatin Bibiya A Kano
  • Wang Yi Ya Bayyana Ra’ayin Sin Kan Yadda Za A Karfafa Huldar Cude-Ni-In-Cude-Ka A Duniya
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Gwamnatin Niger Ta Hana Yan Najeriya Dauke Da Passpor Ta Na ECOWAS Shiga Kasar