Masu Fama Da Cutar Daji Sun Bukaci Gwamnatin Kano Basu Tallafi
Published: 5th, February 2025 GMT
Kungiyar masu fama da cutar daji ta Najeriya reshen jihar Kano, ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta bullo da tallafin kula da cutar a dukkan asibitocin gwamnati.
Shugaban kungiyar Salisu Yusuf ne ya yi wannan kira a yayin wani taron manema labarai na bikin ranar cutar Daji ta duniya tta shekarar 025.
Ya bukaci gwamnati da ta hada gwajin cutar Kansa, da jiyya, da kula da lafiyar jiki a cikin shirinta na ba da tallafin iwon lafiya.
Acewarsa matakin zai rage wa majinyata matsalar kudi, musamman wadanda suka fito daga iyalai masu karamin karfi.
Bugu da kari, kungiyar ta bukaci da a saka masu fama da cutar ta Daji da wadanda suka warke daga cutar a cikin shirin nan na Abba Care da aka kaddamar kwanan nan, wanda ke da nufin tallafa wa mutane masu raunu su 300,000.
Salisu Yusuf ya jaddada cewa cutar Kansa ta kasance babbar lalurar da ke bukatar kulawa cikin gaggawa. “Yawancin mutane na kokawa dangane da biyan kuɗin tantance masu dauke da cutar, da kudaden cigaba da samun kula da karbar magani idan aka gano suna dauke da cutar.
Kungiyar ta masu fama da cutar daji ta Najeriya ta yabawa kokarin gwamnatin jihar na inganta fannin kiwon lafiya, tare da yin kira ga masu hannu da shuni, da kungiyoyi masu zaman kansu, da cibiyoyin kiwon lafiya masu zaman kansu, da su tallafawa shirin kula da cutar Daji a Kano.
Ta jaddada kudirinta na bayar da shawarwarin sauye-sauyen tsarin da ke ba masu fama da cutar Kansa fifiko a Kano, ta hanyar wayar da kan jama’a da shirye-shiryen gano cutar da wuri.
Taken ranar Ciwon Daji ta Duniya na 2025, “United by Unique,” yana nuna mahimmancin aikin gamayya wajen yaƙar cutar Kansa.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ranar Cutar Daji Ta Duniya masu fama da cutar da cutar Daji cutar Kansa da cutar da
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
A zantawa ta water tarho ministocin harkokin waje na kasashen Iran da Turkiya sun bukaci kasashen musulmi su magance matsalar jinkai da kayakin agaji na Falasdinawa a kasarsu da aka mamaye.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Hakan Fidan na kasar Turkiya da tokwaransa na kasar Iran Abbas Aragchi suna fadar haka a jiya Litinin.
A lokacinda yake Magana a kan rikicin da ke faruwa a kasar Turkiyya Abbas Aragchi ya bayyana cewa, rikici ne na cikin gida, kuma yana fatan gwamnatin kasar zara iya magancece ta yadda ta ga ya dace, kuma yana da imani zata iya magance matsalar.
Aragchi ya kara da cewa, wannan shi ne matsayin iran a cikin al-amuran da ke faruwa a kasashen yankin, ya kuma bayyana muhimmancin mutunta al-amuran da suka shafi cikin gida na ko wace kasa a yankin.
Sai kuma Hakan Fidan ministan harkokin wajen Turkiya wanda ya sake jadda matsayin kasarsa wajen neman hanyoyin diblomasiyya don warware matsalolin al-amuran Falasdinu da kasashen yankin da kuma sauran kasashen duniya.