Kungiyar Hizbullah ta fitar da wani bayani a jiya Talata da ta yi Allawadai da takuhkumin da kasar Australia ta kakaba wa babban sakatarenta Sheikh Na’im Kassim.

Bayanin na kungiyar Hizbullah ya kunshi cewa; Matakin, yana sake nuni ne da hakikanin fuskar wannan kasa da a kowace rana take tabbatar da cewa, ita makami a hannun Amurka da Isra’ila.

Hizbullah ta kuma bayyana matakin da cewa na zalunci ne wanda bai jingina da kowane irin dalili na shari’a da halayyar kwarai ba, yana nuni ne kai tsaye da cewa; Suna goyon bayan HKI ne da kuma kare laifukan da take tafkawa da ta’addancinta, tare da yin kira cewa kamata a yi ace kasar ta Australia da ta dauki matakai ne na ladabtarwa akan ‘yan sahayoniya makasa, ta kuma kasance a tare da wadanda ake zalunta a Lebanon da Falasdinu.

Bayanin ya kuma ce: Duk duniya ta ga yadda abokan gaba ‘yan sahayoniya su ka rika yin kisan kiyashi da laifukan yaki akan wadanda ba su ji ba su gani ba a Gaza da kuma Lebanon, don haka duniyar ta san wanene dan ta’adda na hakika, da kuma wanda yake yin kisan kiyashi da tafka laifukan yaki.

Haka nan kuma bayanin ya ce, duniya ta kuma san su wanene suke bayar da kariya ga ‘yan mamaya a siyasance, yake kuma yin tarayya da ita a kisan kiyashin da take yi.

Sai dai kungiyar ta Hizbullah ta ce, wannan matakin babu yadda zai yi tasiri akan ‘yan gwgawarmaya a cikin Lebanon, ko kuma akan matakan da Hzibullah take dauka na kare kasa da al’umma da kuma kasancewa a tare da al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe

A ƙoƙarinta na tallafa wa marayu da mabuƙata, gidauniyar Zakkah da Wakafi a Gombe ta raba wa yara marayu da mabuƙata 100 kayan Sallah.

Da yake jawabi a lokacin rabon tufafin, Shugaban gidauniyar, Amir Abdullahi Abubakar Lamido, ya ce al’adar gidauniyar ce ta riƙa zaƙulo mabuƙata tare da tallafa musu musamman a lokutan bukukuwan Sallah.

An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe

Ya bayyana cewa, a da can gidauniyar na karɓo tsoffin tufafi daga hannun masu hannu da shuni, tana tsaftacewa tare da sake ƙunshe su kafin rabawa.

Amma wannan shekarar, gidauniyar ta ɗauki sabon tsari na sayan sababbin tufafi daga matan da ta koyar da sana’o’in hannu.

Waɗannan mata da suka samu horo a sana’o’i irinsu ɗinki, haɗa sarƙa da abun wuya na mata, da kuma ƙera takalma sun samu damar sayar wa gidauniyar kayayyakin da suka ƙera.

Lamido ya ce wannan hanya ba wai kawai ta amfani da tufafi don marayu da mabuƙata ba, har ma ta ba wa mata damar ƙarfafa musu gwiwa  kan kasuwanci.

Lamido ya yi kira ga masu hannu da shuni su karkatar da zakkar su zuwa ga Zakkah da Wakafi tare da tabbatar musu cewa gudunmawarsu za ta isa ga waɗanda suka cancanta.

Ya ƙara da cewa, da dama daga cikin masu ba da gudummawa sun nuna gamsuwa da yadda gidauniyar ke gudanar da ayyukanta cikin gaskiya da tasiri.

Bayan rabon tufafin Sallah, gidauniyar ta kuma tallafa wa mata guda 75 da jari na ₦15,000 kowannensu.

Waɗannan mata sun samu horo kan yadda za su sarrafa kuɗin su da kyau, ciki har da tanadin kaso ɗaya bisa uku na ribar su a cikin asusu na musamman na tsawon shekara guda don ƙarfafa kasuwancin su ya dore.

Sakataren Jama’atu Nasril Islam (JNI), Saleh Danburan, ya yaba wa gidauniyar bisa ƙoƙarinta na taimakon al’umma tare da kira da ta ci gaba da tsayawa kan turbar addinin Musulunci.

Fitaccen malamin addini musulunci Malam Bello Doma, ya jinjina wa ayyukan gidauniyar tare da bayar da shawarar kafa wani bankin al’umma don bayar da rance marar riba cikin sharuɗa masu sauƙi.

A cewarsa, wannan zai samar da taimakon kuɗi ga al’umma ba tare da kunyata su ko ƙin karɓar buƙatunsu ba yayin da suka nemi taimako.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • Hamas : Isra’ila ta yi amfani da sulhu wajen tattara bayanai kan shugabannin Hamas domin kashe su
  •  Syria: Isra’ila Ta Kai Hari A Kan Sansanin Soja A Yankin Dar’a
  •  Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa