HausaTv:
2025-03-25@17:57:53 GMT

Amnesty Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Kama Benjamin Netanyahu

Published: 5th, February 2025 GMT

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta kira yi Amurka da ta kama Fira ministan “Isra’ila” Benjamin Netanyahu da yake ziyarar aiki a kasar.

A wasu jerin sakwanni da kungiyar ta kare hakkin bil’adama ta duniya ta wallafa a shafinta na X, ta bayyana cewa; Yadda Amurka ta karbi bakuncin Benjamin Netanyahu alhali ana zarginsa da manyan laifuka, yana nuni da cewa ta raina kotun ta kasa da kasa.

Har ila yau kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa ta kuma kara da cewa; Gwamnatin da ta gabata ta Amurka a karkashin Joe Biden ta yi watsi da duk wani yunkuri na shimfida adalci a duniya, kuma shi ma shugaba Trump abinda yake yi kenan a yanzu.

Wannan ce ziyara ta farko da Fira ministan HKI  Benjamin Netanyahu ya kai zuwa waje, tun bayan da kotun kasa da kasar ta fitar da sammacin kamo shi, saboda aikata manyan laifuka da su ka hada da kisan kiyashi.

A ranar 21 ga watan Nuwamba 2024 ne dai kotun kasa da kasa ta fitar da sammacin a kamo Benjamin Netanyahu da ministansa na yaki Yoav Gallant, saboda laifukan da su ka tafka a Gaza.

A karshe kungiyar kare hakkin bil’adaman ta ce, bai kamata ba  a bai wa masu aikata laifukan yaki akan bil’adama  mafaka.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kare hakkin bil adama Benjamin Netanyahu

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet

Jagoran ‘yan adawar Isra’ila Yair Lapid ya yi kira da a gudanar da zanga-zangar gama-gari idan Firaministan kasar Benjamin Netanyahu ya ki bin hukuncin da kotun kolin kasar ta yanke na dakatar da matakin da gwamnatinsa  na korar shugaban hukumar tsaron cikin gida ta Shin Bet.

 Yair Lapid ya shaidawa dubban masu zanga-zanga a Tel Aviv cewa “Idan har gwamnatin 7 ga watan Oktoba ta yanke shawarar kin yin biyayya ga hukuncin kotun, to za ta zama haramtacciyar gwamnati a wannan rana.”

“Dole ne tattalin arzikin kasar ya tsaya cik, majalisa ta shiga yajin aiki, kotu ta shiga yajin aiki, hukumomi su shiga yajin aikin, ba jami’o’i kadai ba, har da makarantu.” Inji shi.

A ranar Juma’a ne Kotun kolin Isra’ila ta dakatar da matakin da gwamnati ta dauka na korar shugaban Shin Bet, Ronen Bar, wanda ba a taba ganin irinsa ba, wanda sanarwar korar tasa ta sake haifar da baraka a tsakanin al’umma.

Amma Netanyahu ya dage kan cewa,”Ronen Bar ba zai ci gaba da zama shugaban Shin Bet ba, ba za a yi yakin basasa ba, kuma Isra’ila za ta ci gaba da kasancewa a matsayin kasa ta dimokuradiyya,” in ji shi a cikin wani sakon bidiyo inda yake kalubalantar Kotun Koli.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lauyoyi 77 a Jamus sun yi kira ga gwamnati da ta mutunta sammacin ICC na cafke Netanyahu
  • Yawan Ziyarar Da ‘Yan Siyasa Da ‘Yan Kasuwar Amurka Ke Kawowa Sin Ya Zo Da Mamaki
  •  Jam’iyyar “Turkish National Party” Ta Tsaid Imam Uglu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa
  • Dokar Ta-ɓaci A Ribas: Gwamnonin PDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli
  • NDLEA Ta Kama Ƴar Indiya Ɗauke Da Hodar Iblis A Kano
  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Dole Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Ta Daina Barazana Ga Masu Sukar Ta – Amnesty
  • Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet
  • Amurka ta cire tukuicin wanda ya bayar da bayani kan mataimakin shugaban Taliban
  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Game Da Tunanin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam Da Kin Amincewa Da Siyasantar Da Hakkin Dan Adam