Rahotanni  sun ambaci cewa bayan ficewar sojan Faransa na karshe daga sansanin Abaci dake gabacin kasar Chadi,kasar Turkiya tana shirin maye gurbinta.

Wata majiyar kasar Turkiya ta shaidawa wata kafar labaru ta Afirka cewa, Ankara tana shirin girke jiragen yaki marasa matuki a cikin sansanin dake kan iyaka da kasar Libya akokarin da take yi na cike gurbin da Faransa ta bari, da zummar tabbatar da kanta a cikin wanann yankin na Afirka.

Gwamnatin Chadi ta bai wa Turkiya sansanin na Abaci a karkashin yarjejeniyar da kasashen biyu su ka cimmawa a tsakiyar watan da ya gabata,bayan doguwar tattaunawa da aka yi a tsakanin jami’an gwmanatocin kasashen biyu.

Haka nan kuma rahoton ya ce, kasar Turkiya ta bai wa gwamnatin kasar ta Chadi jiragen sama marasa matuki samfurin Beyraghdar. Haka nan kuma da akwai masu bayar da shawara na soja da dama daga kasar ta Turkiya a cikin kasar ta Chadi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Thomas Friedman: Trump Yana Son Ci Gaba Da Zama Shugaban Kasar Amurka Har Abada

Fitaccen dan jarida na Amurka wanda  Patrick Heili ya yi hira da shi ta  Podcast, ya bayyana cewa; Shugaban kasar Amurka Donald Trump yana son ya ci gaba da zama akan kujerar mulki har abada.

Hirar da Thomas Friedman ta mayar da hankali ne akan salon mulkin Donald Trump da yadda yake son sauya yadda Amurka take a cikin kwanaki 100 na farkon mulkinsa.

Thomas Friedman ya ya bayyana yadda shugaba kasar ta Amurka Donald Trump yake kokarin kwaikwayon salon mulkin shugaban kasar China Xi Jin Ping da kuma na kasar Rasha Vladmir Putin da Fira ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu.

Shi kuwa mai gabatar da shirin  Patrick Heili ya yi ta’aliki da cewa, Trump yana kallon wadannan shugabannin a matsayin masu karfi a cikin duniyar da take cike da raunana, kuma shi Donald Trump yana son ya shimfida ikonsa a cikin duniya baki daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Thomas Friedman: Trump Yana Son Ci Gaba Da Zama Shugaban Kasar Amurka Har Abada
  • Malamai Na Karbar Horo Akan Shirin Ilimin Mata Na AGILE a Jigawa
  • MDD Ta CE Sake Tada Komatsar Tattalin Arzikin Kasar Siriya Zau Dauki Shekaru 50 Nan Gaba
  • Wang Yi Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Uganda
  • Jakadan Sin Dake Najeriya Ya Gana Da Karamar Ministar Harkokin Wajen Kasar
  • Hamas Za Ta Saki Dukkan Fursunonin Isra’ila Da Ke Hannunta
  • Turkiya Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Sulhu Tsakanin Habasha Da Somaliya
  •  Rasha Ta Kakkabo Jiragen  Sama Marasa Matuki 9 Na Kasar Ukiraniya
  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri
  • Gwamnatin Niger Ta Hana Yan Najeriya Dauke Da Passpor Ta Na ECOWAS Shiga Kasar