HausaTv:
2025-03-25@08:13:33 GMT

 Politico: Sojojin Ukiraniya Suna Fuskantar Matsin Lamba Da Karancin Mayaka

Published: 5th, February 2025 GMT

Jaridar Politico ta buga wani rahoton dake cewa sojojin kasar Ukiraniya suna fuskantar matsin lamba mai yawa, da kuma rashin kwararrun mayaka.

Wannan matsin lambar da sojojin kasar suke fuskanta ya sa ana tunanin mayar da sojojin sama zuwa na kasa da tura su filin daga. Har ila yau jaridar ta ambaci yadda sojojin da suke guduwa daga filin yaki suna karuwa.

Jaridar ta kuma kara da cewa; Babban hafsan hafsoshin kasar ta Ukiraniya ya bayar da umarnin a dauki sojojin sama 5000 a mayar da su na kasa.

Da akwai tsoron cewa kasar ta Ukiraniya tana rashin kwararrun sojojinta, da ba za ta iya maye gurbinsu a cikin sauki ba idan har aka tura su zuwa filin daga.

A gefe daya, ministan harkokin wajen kasar ta Amurka Marco Rubio ya bayyana cewa; A halin yanzu Ukiraniya tana yin asarar mutanenta ba wai kudi ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Jam’iyyar “Turkish National Party” Ta Tsaid Imam Uglu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa

Jami’iyyar adawa ta “Turkish National Party” ta bayyana cewa dan takararta a zaben shugaban kasa na 2028 shi ne magajin garin Istanbul Akram Imam Ugulu wanda a halin yanzu yake a gidan kurkuku.

Imam Uglu dan shekara 53 shi ne muhimmin dan takarar shugaban kasa a tsakanin ‘yan hamayya da ake hasashen cewa  zai iya bugawa da shugaba Rajab Tayyib Urdugan a zabe mai zuwa.

‘Yan jam’iyyar ta adawa sun kada kuri’ar tsayar da Imam Ugulu a matsayin dan takararsu a zabe mai zuwa, inda ya sami kuri’u miliyan 1.6 a tsakanin miliyan 1.7.

Shugaban jam’iyyar ta “National Party” Uzgur Uzil wanda ya sanar da hakan, ya kuma bayyana cewa an yi zabe na gwaji da miliyoyin mutane su ka zabi Imam a matsayin shugaban kasa.

Kasar Turkiya ta fada cikin dambaruwar siyasa ne bayan da aka kama ‘yan hamayyar siyasa kusan 100 da aka zarga da cin hanci da rashawa, da kuma taimakawa ta’addanci. Daga cikin wadanda aka kama da akwai Akram Imam Uglu wanda shi ne magajin garin Istanbul.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Syria: Isra’ila Ta Kai Hari A Kan Sansanin Soja A Yankin Dar’a
  •  Jam’iyyar “Turkish National Party” Ta Tsaid Imam Uglu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Karfafa Gwiwar Kamfanonin Kasashen Duniya Da Su Fadada Zuba Jari A Sin 
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • Al-Huthi Ya Ce Kawo Wani Jirgin Ruwa Mai Daukar Jiragen Saman Yaki Gazawa Ce Ga Amurka
  • Amurka ta sake kai hare-hare Yemen
  • Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum
  •  Haaretz: Sojojin Isra’ila Suna Kan Shirya Kai Wa Gaza Hari Ta Kasa
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
  • Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024