DRC: Kungiyar M23 Ta Shelanta Tsagaita Wutar Yaki A Garin Goma
Published: 5th, February 2025 GMT
Kungiyar ‘yan tawaye ta M 23 ta sanar da tsagaita wutar yaki a garin Goma da take rike da shi, saboda dalilai na jin kai.
Kungiyar wacce take samun goyon bayan kasar Rwanda wacce ta kwace iko da birnin Goma da shi ne birni mafi girma a gabashin wannan kasa, ta sanar da tsagaita wutar yaki ta gefe daya saboda abinda ta kira samar da damar gudanar da ayyukan agaji.
Kungiyar ta ce, ta amince da tsagita wutar yakin ne domin amsa kiran da aka yi dangane da hakan, saboda a taimaka wa dubun dubatar mutanen da suke a tarwatse saboda yaki.
Ya zuwa yanzu dai babu wani furuci da ya fito daga gwamnatin kasar DRC akan batun tsagaita wutar yakin.
A ranar Litinin din da ta gabata kakakin MDD Stephane Dujarric ya yi bayani akan halin da ake ciki a kasar ta DRC tare da nuna damuwa akan matsalolin kiwon lafiya a cikin kasar.
Wani rahoto na MDD ya bayyana cewa, mutane 900 ne su ka rasu a cikin kasar ta DRC, yayin da wasu 2,880 su ka jikkata sanadiyyar tashe-tashen hankulan na bayan nan.
Daga farkon wannan shekara ta 2025, fiye da mutane 400,000 ne su ka bar matsugunansu a cikin kasar, kamar yadda hukumar MDD mai kula da ‘yan hijira ta bayyana.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
Jiragen yakin HKI sun harba makamai masu linzami guda biyu akan ginin asibitin Ma’amadani dake Gaza. Harin ya yi sanadiyyar rushewar wasu bangarori da su ka hada dakunan yin gwaje-gwaje da kantin sayar da magani.
Saboda hare-haren na Isra’ila a wannan asibitin, da akwai gwamman marasa lafiya da suke kwance a kasa a waje, yayin da wasu kuma suke kwance wajen asibiti.
Kungiyar Hamas ta bayyana harin da sojojin HKI su ka kai wa asibitin da cewa wani sabon laifi ne na dabbanci da ‘yan sahayoniyar suka tafka a Gaza.
Haka nan kuma Kungiyar ta Hamas ta zargi Amurka da cewa ita ce take bai wa HKI haske akan tafka laifukan da take yi a Falasdinu.
Bugu da kari kungiyar ta Hamas ta kuma yi mamaki akan yadda kungiyoyin kasa da kasa da su ka hada da MDD suke yin shiru akan laifukan da ake tafkawa da ba su da tamka a wannan zamanin, akan asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya da cutar da marasa lafiya da korarsu daga asibiti zuwa kan tituna.