Aminiya:
2025-02-22@06:24:55 GMT

Hausawa sun yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri

Published: 5th, February 2025 GMT

A kwanakin baya Hausawa mazauna Jahar Imo suka yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri Fadar Gwamnatin Jihar Imo da ke yankin Kudu maso Gabas yankin da ake kira da Ibo.

Hausawa mazauna Jihar Imo da ke Owerri babban birnin jahar a kwanan baya sun yi bikin cika shekara 153 da zuwa Owerri, Jahar Imo da zama domin gudanar da harkokin na kasuwanci.

DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’ Sarki Sanusi ya ziyarci unguwar da mutane suka rasu a dalilin rusau

Yawancin garurukan Asaba da Benin da Obudu a Jihar Kuros Riba su ne mazaunin Hausawa na farko a Jahar Kuros Riba sai kuma garin Alele a Jihar Ribas mai iyaka da Jihar Bayelsa da garin Fatakwal da sauran wasu garuruka a Kudu maso Kudu da garin Anaca Jahar Anambra.

Hausawa sun zo garin Owerri tun kimanin shekara 153, wanda akasarinsu Kanawa ne daga garin Tsakuwa da ke Ƙaramar Hukumar Garko da ke Jihar Kano, kamar yadda Sarkin Hausawan Owerri, Alhaji Auwalu Baba Sai’idu Sulaiman ya shaida wa Aminiya.

Masarautar Hausawan kamar yadda Sarkin Alhaji Sai’du Suleiman ya tabbar, tana ƙunshe da ƙabilun Arewacin Nijeriya Musulmi da waɗanda ba Musulmai, suna zaune lafiya tsakaninsu da kuma ’yan asalin jihar.

Ko a gwamnatin da ta shude tsohon Gwamnan Jihar Imo ya naɗa ɗan Arewa muƙamin mataimaki na musamman kan harkokin baki wadanda ba ’yan asalin jihar ba.

Ta bangaren ci gaba da bmazauna Jahar Imo da kuma babban birnin Owerri, Sarkin ya ci gaba da cewa, “Wannan masarauta tana da hakimi guda da dagaci guda da ke kowace karamar hukuma da ke Jihar Imo guda 27 da ke daukacin kananan hukumomin 27 na Jihar ke nan.”

Da yake karin haske game da masarautar, kakakin Sarkin, Nura Bala Ajingi ya ce, masarauta ta faɗaɗa ne zuwa sauran kananan hukumomin da aka ambata saboda ci gaban da ake samu na al’ummar Arewa mazauna jahar a karkashin wannan masarauta da Alhaji Auwal Baba Sa’idu ke shugabanta.

Haka nan kuma sarkin Hausawa Owerri shi ne sakataren sarakunan daukacin majalisar sarakunan Hausawa mazauna shiyyar Kudu maso Gabashin Nijeriya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hausawa Jihar Imo Jihar Kano shekara 153

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano

Wata gobara da ta tashi cikin dare a garin Satigal da ke Ƙaramar Hukumar Bunkure a Jihar Kano, ta ƙone gidaje da dama, dabbobi, da rumbunan ajiyar hatsi guda shida.

Sai dai kawo yanzu babu labarin rasa rai a gobarar.

Ukraine ce mai laifi a yaƙin da ta ke yi da Rasha — Trump Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan Tsaro

A cewar wata sanarwa da Jami’in Yaɗa Labarai na shiyyar Rano, Rabi’u Kura, ya fitar, mazauna yankin sun haɗa kai wajen kashe gobarar da kuma ceton rayuka da dukiyoyi.

Bayan haka, an kai rahoton lamarin ga Sarkin Rano, Dokta Muhammad Isa Umaru, a fadarsa.

Hakimin Satigal, ya jagoranci wasu mazauna yankin zuwa wajen sarkin, inda suka bayyana cewa gobarar ta lalata gidaje guda shida, kaya, hatsi, dabbobi da kuma wasu kayayyakin amfanin yau da kullum da darajarsu ta kai ta miliyoyin Naira.

Rahotanni sun nuna cewa gobarar ta fara ne sakamakon wuta da aka yi amfani da ita wajen dafa abinci, amma aka bar ta ba tare da an kashe ba.

Sarkin ya jajanta wa waɗanda abin ya shafa kuma ya ba su tallafin Naira 200,000 domin rage musu raɗaɗin asarar da suka yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Dauki Nauyin Dalibai 80 Da Ke Manyan Makarantu
  • Kasar Sin Ta Bukaci G20 Ta Zama Karfin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Duniya
  • Kungiyar Wasan Kareti Ta Iran Ta Zama Gwarzo A Asyia
  • Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu
  • An Jinjinawa Kwarewar Sin A Bikin Nune-Nunen Ayyukan Gona Na Cote d’Ivoire
  • Hisbah ta rufe gidajen rawa a Katsina
  • Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano
  • Tinubu Ya Taya Babban Mai Tace Labarai Na LEADERSHIP, Ishiekwene Murnar Cika Shekaru 60
  • Sarkin Qatar Ya Iso Tehran A Yau Laraba
  • Sojojin Sudan Sun Killace Fadar Shugaban Kasa Da Take A Hannun ‘Yan Tawayen A Birnin Khartum