Aminiya:
2025-02-22@06:34:12 GMT

An soma rigimar haraji tsakanin China da Amurka

Published: 5th, February 2025 GMT

A bayan nan ne Amurka ta sanya harajin kashi 25 a kan kayayyakin da ake shigar wa ƙasar daga Canada da Mexico da kuma kashi 10 kan kayayyakin makamashi na Canada, yayin da kayayyakin China za su fuskanci harajin kashi 10.

Sakatariyar yaɗa labaran Fadar White House, Karoline Leavitt, ce ta bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai a ranar Juma’a.

Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zabo Hausawa sun yi bikin cika shekara 153 da zama a garin Owerri

Ta bayyana cewa “Canada da Mexico suna ba da damar shigar da muguwar ƙwayar nan ta fentanyl da ke kashe Amurkawa da kuma baƙin haure ba bisa ka’ida ba zuwa kasar mu.”

Ta ce Shugaba Donald Trump ya ba da umarnin wanda zai soma aiki daga ranar Talata, domin magance matsalar shigar da maganin kashe raɗaɗi na fentanyl da matsalar ‘yan gudun hijira da ke shiga Amurka ba bisa ƙa’ida ba.

“Shugaba Donald Trump na ɗaukar ƙwararan matakai don kare Amurkawa daga matsalar maganin na fentanyl. Fentanyl shi ne kan gaba wajen sanadin mutuwar Amurkawa masu shekaru 18 zuwa 45,” in ji Leavitt.

Amurkan dai ta zargi masu safarar miyagun ƙwayoyi na Mexico da kasancewa “kan gaba a duniya wajen safarar” fentanyl da sauran ƙwayoyi, yana zargin akwai ƙawance tsakanin masu safarar da gwamnatin Mexico.

Game da Canada, Fadar White House ta yi ƙarin haske game da ƙaruwar samar da maganin na kashe raɗaɗi na fentanyl da kuma tsallaka wa da shi kan iyaka ba bisa ƙa’ida ba, tana mai cewa: “an kama fentanyl a kan iyakar Arewa a bara wanda zai iya kashe Amurkawa miliyan 9.8.”

An soki China saboda zargin tana taka rawa wajen bayar da tallafi ga kamfanonin sinadarai wajen fitar da fentanyl zuwa ƙasashen waje, inda Fadar White House ta yi iƙirarin cewa: “ba wai kawai China ta gaza wajen daƙile tushen haramtattun ƙwayoyi ba, har ma tana taimaka wa wannan kasuwanci.”

Martanin Canada da Mexico

Ƙasashen Canada da Mexico sun sanar da ɗaukar matakan ramuwar gayya kan harajin da Shugaba Trump ya ɗora wa kayayyakinsu.

A ranar Asabar, Firaminista Justin Trudeau ya ce Canada za ta sanya harajin kashi 25 kan kayayyakin Amurka da suka kai dala biliyan 106.5 a matsayin martani ga harajin Amurka.

Harajin dala biliyan 20 zai fara aiki daga ranar Talata, sannan na dala biliyan 86 zai fara aiki a cikin kwanaki 21, kamar yadda Trudeau ya shaida wa wani taron manema labarai.

Trudeau ya yi gargaɗin cewa harajin zai cutar da Amurka, wacce daɗaɗɗiyar ƙawar ƙasar ta Canada ce.

Ya nemi mutanen Canada su riƙa sayen kayayyakin da aka yi a ƙasar, kuma su riƙa gudanar da hutu a gida maimakon a Amurka.

Ya ce ana kuma duba wasu matakan da ba na haraji ba, da suka haɗa da wasu da suka shafi ma’adanai masu mahimmanci da sayen makamashi da sauran ɓangarorin haɗin gwiwa.

Trudeau ya kuma ƙara da cewa, ƙasashen Canada da Mexico suna aiki tare don fuskantar harajin da Washington ta ɗora wa kayayyakinsu.

Fadar White House ta ce manufar harajin ita ce matsa wa Mexico da Canada da China lamba su ƙara ba da haɗin kai kan daƙile shigar da miyagun ƙwayoyi da tsaron kan iyakoki da hana kwarar baƙin haure shiga ƙasar ta ɓarauniyar hanya.

China ta bi sahu

China a wani mataki na ramuwar gayya ta lafta wa Amurka harajin kaso 15 cikin 100 na kayayakin kwal da na makamashin gas da ake shigar da shi kasar daga Amurka.

Ƙarin harajin a cewar Ma’aikatar Kuɗin Beijing zai fara aiki ne a makon gobe.

A cikin sanarwar da ta fitar ta ɗaukar matakan ramuwa, China ta zargi Amurka a ƙarƙashin Donald Trump da karya ƙa’idojin kasuwanci na ƙasa da ƙasa.

“Gaban kai da Amurka ta yi ita kaɗai ta lafta haraji ya saɓa ƙa’idojin Hukumar Kasuwaci ta Duniya. Wannan ya saɓa wa yarjeniyoyin kasuwanci da tattalin arziƙi tsakanin China da Amurka.”

Bugu da ƙari China ta sanar matakin fara bincike a kan kamfanin fasaha na Google.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fadar White House

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa. Sirar Imam Alhassan (a) 19

19-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa Shirin wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane rastan na shahid Aya. Murtadha muttahhari, ko cikin littafin Mathnawi na maulana jalaluddeen, Rumi, ko kuma cikin wasu littafan. Da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.

///… Madalla, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Alhassan (s) Jikan manzon All..(s) sannan limami na 2 daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s) kuma da, na farko ga  Fitima(s) diyar manzon All..(s).

A cikin shirimmu da ya gabata, mun kawo maku yadda aka zabi Khilifa na farko da kuma yadda wasu daga cikin sahabban manzon All..(s) suka ki amincewa da bai’at tasa.

Na gaba-gaba daga cikin wadanda suka ki yi masa bai’a shi ne Amirulmuminina Aliyu dan Abitalib (a), sannan akwai Sa’adu dan Ubada, shugaban kabilar Hazraju daga cikin Ansar, sannan minji makomar sa a lokacinda aka tsinci gawarsa a cikin wata rijiya a hanyar sha.

Sannan mu fara kawo mauki dalilai da hujjoji wadanda Imam Ali (a) da kansa ya gabatarwa Khalifa na farko dangane da cancantarsa, da hakkinsa na kujerar Khalifanci bayan wafatin manzon All..(s).

Imam Ali (a) bayan an yiwa Abubakar dan Abu Kuhafa, bai’a a matsayin Khalifan manzon All..(s),  ya nuna bacin ranasa ya kuma bayyana rashin amincewarsa, ya na ganin hakkinsa ne ya kwace, kuma ya bukaci a mayar masa da hakkinsa.

Malaman tarihi sun bayyana cewa Amirulmuminina Aliyu dan Abitalib (a) ya kafa hujjoji da dama don dawo da hakkinsa daga hannun Abubakar.  Wannan ya faru ba sau guda ba, inda a cikinsu gaba daya, ya bayyana masu shi ne mai hakki, saboda matsayinsa a cikin musulmi, shi ne na farkon musulunta, ya fi dukkan sahabbai ilmi, ya kasance jarumi a mafi yawan yake-yaken musulunci.

*-Da farko, a lokacinda aka kama shi daga cikin gidansa, a dabaibaye cikin igiyoyi aka kawo shi masallaci a gaban Abubakar, sai aka ce masa kayi wa Abubakar bai’a, sai ya basu amsa,  al-hali yana dabaibaye cikin igiyoyi. (Ni nafi cancanta da ku yi mani bai’a, b azan yi maku bai’a ba. Na fi cancanta ku yi  mani bai’a. Kun karbi wannan al-amarin daga Ansaru, kun hujjacesu da kusanci da manzon All..(s). Sannan kun karbeshi daga iyalan gidan manzon All..(s) da karfi. Shin baku fadawa Ansar  kan cewa ku ne makusantar manzon All…S ba, kun ce ku kuka fi cancanta da wannan al-amari, tunda manzon All..yana fito ne daga cikinku ba, sai suka mika maku wuya. Suka sallama maku shugabanci?. Don haka nima ina hujjace ku da abinda kuka hujjace Ansar da shi, kan cewa mu muka fi cancanta da al-amarin manzon All..(s) a raye da kuma bayan mutuwarsa….) don haka amirulmuminina ya shiga ta hanyar da Muhajirun suka bi wajen kwace hakkinsa, y ace masu, abinda kuaka fada faskiya ne, ammma ni kuma ina kafa maku hujja kan cewa mu munfi kusa da manzon All..(s) kanku, ku mika mana shugabancimmu mu.

Idan a dangantaka ne, shi dan’ammin manzon All.. kuma surukinsa ne da hanyar diyarsa Zahra’ (s).

A lokacinda dankhaddani ya ji wannan hujjar sai ya fito ta wata hanyar, ta nuna karfi, inda yace baza’a barkaba sai kayi bai’a

Sai Imam Ali ya daga murya, yana cewa masa: (Ka tasha masa, ka na da rabinsa. Ka rike masa al-amari a yau sai ya mayar maka da shi gobe.}

Sai Imam (a) ya kara da cewa: Na rantse da All..Ya Umar b azan karbi zancenka ba, kuma ba zanyi bai’a ba.).

Sai Abubakar ya ji tsoro kan abinda karshensa ba zai yi dadi ba, sai ya zo kusa da Aliyu (a) yana cewa: Idan kaki kayi bai’a ba zama tilasta maka ba.

A wani bangare kuma Ubu ubaida dan Jarra, yayi kokarin gamsar da Imam yayi bai’a a hankali, sai y ace masa: Ya dana mmi na, kai shekarunka kadanne, wadannan dattawan mutanenka ne, baka da korewa da kuma sanin al-amura kamarsu ba. Ni bana ganin face, Abubakar ya fika sanin al-amura fiye da kai. Ya fika sani da kuma gogewa a kansa. Ka sallamawa Abubakar wannan al-amari, don lalle idan ka yi tsawon rai, kai ka cancanci wannan matsayin, saboda falalarka, da adininka da kuma ilminka. Sannan ga kusancinka, da suurukantakarka, da kuma da saurin fahintarka da kuma kekyawar matsayinta a tarinin addinin musulunci. ..}

Magabar Abu Ubaida dan jarrah, ya ingiza Imam (a) yana magana wa, dukkan muhajirun ya na fadar abubuwanda All…ya fifita iyalan gidan manzon All..(s) da su. (Ina hadaku da All..ina hadaku da All..ya ku masu hijira, kada ku fitar da shugabancin Muhammadu a cikin larabawa daga gidan shi. Daga tsakiyar gidansa, ku maida shi gidajenku, a kuma tsakiyar gidajenku. Kada ku tumbuke iyalan gidansa daga matsayinsa a cikin mutane da kuma hakkinsa.

Na ranste da All..ya ku muhajirun wallahi mu muka fi cancanta da wannan al-amarin da ku, – don mu iyalan gidansa-saboda wadanda suka kasance masu karatun al-kur’ani cikimmu, da ilimin sanin addini, da kuma masana sunnar manzon All..(s), da kuma sanin al-amuran Jagoranci, da kuma mai tunkude wa al-umma mummunan abinda ke tunkararsu, kuma wanda zai yi rabo a tsakaninsu dai-dai,(babu nuna fifiko). Wallahi lalle – mai wadannan sifofi yana cikimmu- kada ku bi son zuciya ku bace daga tafarkin All..sai ku kara nisanta daga All…),

Da wannan khudunar Imam (s) ya tunkudewa mutanen duk wata shubha, bai bar masu wata kofa face ya rufe ta, da wannan khuduba mai fasaha da kuma bayyana gaskiya.

Wannan kuma ya ture duk abinda Ubu ubaida dan jarra ya yi riko da shi don kare Abubakar a kan abinda yake kai, na cewa shi ne yafi amirul muminina (a) shekaru.

Imam (s) ya nuna masu cewa, wanda ya mallaki abubuwan da ya ambata din nan sune wadanda ake mizanin shugabanci da su a musulunci. Kuma su ya cancanci zama mai kula da al-amuran musulmi.

Sannan addinin All.., da sanin sunar manzon All..(s) da sanin makamar aiki na kula da al-amuran mutane, da tunkede masu mummuna, da rabo tsakaninsu da adalci, wadannan sune sifofinda musulunci yake kula da su, a matsayin abin lura wajen kuma ba wanda yake da wadannan sifofi sai a cikin iyalan gidan manzon All…(s). wannane ya sa suka kasance, wadanda suka fi cancanta da wannan al-amari fiye da kowa.

Har’ila yau Zahra’u (s) shugaban matan Aljanna ta hujjacesu da wasu hujjojin kwarara, kan mumunan abinda ta aikata, da babban laifin da suka aikata. Tana fada (s) a cikin wata khudubarta kan cewa:

Kaitonku, ina suka kaita-wato khalifancin-daga barin – makafar annabci, da ginshikan annabcic, masaukar ruhun Ameen. Masanan ilmin adini da duniya, Ku saurar ! wannan shi ne asara babba. Kuma menene suke ganin tawaya ne a wajen baban Hassan? Suna sukansa- wallahi-kaifin takobinsa da kuma tsananin damkarsa.

A cikin khudubar (s) ta gutsurowa musulmi ilmin gaibun da All..ko manzonsa suka sanar da ita. Ta cewa masu zuwa a bayan zasu dandani mummunan aikin da magabata suke. Don haka an haramtawa na baya saboda kurakuran da magabata suka yi.

Da musulmi muminai a cikin sahabban manzon All…(s) sun amince da Amirul muminina (a) a matsayin shugaba a lokacin, da sun ci ta sama da kasa, da kuma karkashin kafafuwansu. Da kuwa basu jawowa al-ummun baya sharrin da musibun da suka fadawa musulmi tun lokacin hzr zuwa yanzu ba.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu wassalamu alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Turji Ya Ƙaƙaba Wa Ƙauyen Mataimakin Gwamnan Sokoto Da Wasu Biyan Harajin Miliyan 22
  • Limamin  Juma’a Na Tehran Ya Jaddada Muhimmancin Hadin Kai A Tsakanin Al’ummar Musulmi
  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa
  • Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu
  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Kara Haraji
  • Turkiya Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Sulhu Tsakanin Habasha Da Somaliya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu
  • Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara
  • Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar
  • Kissoshin Rayuwa. Sirar Imam Alhassan (a) 19