Kasar Afirka Ta Kudu ta ga yadda Palasdinawa suka jajirce wajen kare kansu daga HKI ne, ya sa ta gurfanar da HKI a gaban kutun ICC don kawo karshen kissan kiyashin da yahudawan suke masu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya kara da cewa, kasar Afirka ta gudu dai tana dade tana goyon bayan masu gwagwarmayan neman yencinsu a duniya daga ciki da da kasar Falasdinu da aka mamaye.

Har ila yau da kuma ganin tarihin da kasar take da shi, na yaki da wariyar launin fata a kasar, duk sun hadu sun karfafa ta wajen daukar wannan matakin kan HKI.

Jakadan kasar Afirka ta kudu a nan Tehran, Francis Moloi ne ya fadawa kamfanin dillancin labaran ‘Iran Press’ na kasar Iran a nan Tehran a jiya Talata. Ya kuma kara da cewa, wannan dan kadan Kenan daga abinda kasar Afrika ta kudu za ta iya gabatarwa da karfafa wa al-ummar Falasdinawa.

Yakin gaza dai ya farkar da mutane da dama a duniya gaba daya, kan al-amarin Gaza da kuma yadda  HKI ta ke amfani da dukkan karfinta a cikin watannin 15 da sukagabata don kashe Falasdinawa da kuma rusa yankin nasu gaba daya.

Kasashen duniya musamman ita Afrika ta Kudu ta dauki wannan matakin ne, saboda yadda HKI ta ki mutunta dokokin kasa da kasa, musamman wadanda suka shafi

mutuncin bil’adama da kuma hakkin rayuwa ga Falasdinaw.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Duniya na ci gaba da yin tir da Isra’ila kan dawo da hare-harenta a Gaza

Majalisar Dinkin Duniya da Tarayyar Turai sun ce, tsagaita bude wuta nan take a Gaza ya zama dole.

Da yake magana a wani taron kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, mataimakin babban sakataren majalisar kan  harkokin siyasa Khaled Khari, ya ba da rahoto game da tabarbarewar al’amura a Gaza bayan da Isra’ila ta karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da musayar fursunoni da aka kwashe kusan watanni biyu ana aiki da ita.

“A kowace rana, muna kara nisa daga manufar mayar da sauran mutanen da aka yi garkuwa da su zuwa gidajensu lami lafiya,” in ji Khari, yayin da yake magana kan fursunonin Isra’ila da aka yi garkuwa da su a Gaza.

Babban jami’in kula da harkokin siyasa na Majalisar Dinkin Duniya ya yi kira da a dawo da tattaunawar tsagaita bude wuta da kuma kai kayan agaji a Gaza ba tare da wata tangarda ba.

Ya yi ishara da jawabin da babban jami’in agaji na Majalisar Dinkin Duniya Tom Fletcher ya yi wa UNSC a farkon wannan makon, inda yace yin aiki da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ita ce hanya mafi dacewa domin kare fararen hula  a Gaza, da kuma sako wadanda aka yi garkuwa da su, gami da shigar da kayan agaji da kayayyakin bukatar rayuwa zuwa Gaza.

Khari ya ce jami’an MDD shida na daga cikin daruruwan mutanen da aka kashe tun bayan da Isra’ila ta sake dawo da kai hare-hare a ranar Talata.

A daya bangaren kuma Majalisar Tarayyar Turai ta yi Allah wadai da “rugujewar yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza, wanda ya yi sanadin mutuwa da  jikkatar fararen hula masu yawa a hare-haren jiragen saman Isra’ila a baya-bayan nan”.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da dimokuraɗiyya ta gaza kawo ci gaba a Afirka — Obasanjo
  • Wajibcin Gina Al’ummar Duniya Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya
  • Iran ta yi gargadin cewa keta hurumin Lebanon da Isra’ila ke yi barazana ne ga zaman lafiyar duniya
  • An yi wa Jakadan Afirka ta Kudu da Amurka ta kora tarbar Jamurumai bayan komawarsa gida
  • Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya
  • Duniya na ci gaba da yin tir da Isra’ila kan dawo da hare-harenta a Gaza
  • Iran da Masar sun tattauna kan rikicin da Isra’ila ta jefa yankin gabas ta tsakiya
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  • Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar