Aminiya:
2025-02-21@14:26:21 GMT

NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana

Published: 5th, February 2025 GMT

Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON ta sanar da tsawaita wa’adin karɓar kuɗin aikin Hajjin bana.

NAHCON ta ce daga yanzu zuwa 10 ga watan Fabrairu ƙofa a buɗe take ta ci gaba da karɓar kuɗin kujera ga maniyyatan da ke son sauke farali a bana.

Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba An soma rigimar haraji tsakanin China da Amurka

Ana iya tuna cewa, da misalin ƙarfe goma sha biyun daren ranar Juma’a 31 ga watan Janairun 2025, ne wa’adin biyan kuɗin kujerun aikin hajjin bana ya cika.

Sai dai cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Hukumar NAHCON ta ƙasa, Fatima Sanda Usara ta fitar, ta ce tsawaita wa’adin wata dama ce ga maniyyatan da ba su kammala biyan kuɗin kujerar ba.

Hajiya Fatima ta kuma ce NAHCON ta buƙaci shugabannin hukumomin Alhazai na jihohi da su tabbatar sun bayar da haɗin kai na miƙa mata kuɗaɗen alhazan domin tanadar musu masauki a ƙasa mai tsarki.

Tun bayan cikar wa’adin na farko ne NAHCON, ta shaida wa BBC cewa, idan har akwai wani sabon bayani a game da ƙara wa’adin biyan kuɗin to hukumarsu za ta sanar.

NAHCON ta ce daga bayanan da suke samu daga jihohi kawo yanzu mutane sun biya kuɗinsu domin akwai ma waɗanda suka biya kuɗin da ya zarta wanda aka sanar sakamakon hasashen cewa kuɗin kujerar bana zai iya kai wa Naira miliyan 10.

“Yanzu irin waɗannan mutane da suka biya kuɗin da ya zarta na kujerar suna ta murna bayan sanar da kuɗin kujerar ta bana, kuma nan ba da jimawa ba za a mayar musu da sauran kuɗinsu bayan an cire wanda ya kamata,” in ji Hajiya Fatima.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kuɗin Kujera biyan kuɗin

এছাড়াও পড়ুন:

An Haramta Wa Tankokin Man fetur Da Ke Jigilar Lita 60,000 Zirga-zirga A Faɗin Titunan Nijeriya 

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja a ranar Laraba, Ogbugo Ukoha, Babban Darakta a sashen rarraba mai tare da adanawa na NMDPRA, ya ce matakin ya biyo bayan karuwar firgicin hadurran da ke tattare da manyan motocin dakon man.

 

“Kwamitin fasaha na masu ruwa da tsaki ya gana a yau don cimma wasu muhimman kudurori guda 10 da nufin rage karuwar yawan hadurran tankokin mai da ke janyo asarar rayuka,” in ji Ukoha.

 

An cimma wannan matsaya ne bayan tattaunawa da manyan masu ruwa da tsaki da suka hada da DSS, hukumar kashe gobara ta tarayya, hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC), kungiyar masu sufurin mota ta kasa (NARTO), kungiyar ma’aikatan man fetur da iskar gas ta kasa (NUPENG), hukumar tabbatar da ingancin kayayyaki ta kasa (SON), DAPPRAMAN da NDPRAMAN.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa
  • Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida
  • An Haramta Wa Tankokin Man fetur Da Ke Jigilar Lita 60,000 Zirga-zirga A Faɗin Titunan Nijeriya 
  • An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai
  • Saudiyya ta Gayyaci Kasashen Larabawa Kan Batun Kan Batun Gaza
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2 kan jinkirin biyan kuɗin fansa
  • Gwamnatin Kano Ta Amince Da Biyan Bashin Albashin Ma’aikatan Tsaftar Muhalli 2,369
  • IRGC Ta Sanar Da Rusa  Kungiyar “Yan Leken Asirin Amurka Da HKI A Iran
  • Babban Kwamandan Sojojin Iran Ya Sanar Da Tsarin Sabunta Matakan Mayar Da Martani Kan Makiya