Aminiya:
2025-03-24@01:29:24 GMT

NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana

Published: 5th, February 2025 GMT

Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON ta sanar da tsawaita wa’adin karɓar kuɗin aikin Hajjin bana.

NAHCON ta ce daga yanzu zuwa 10 ga watan Fabrairu ƙofa a buɗe take ta ci gaba da karɓar kuɗin kujera ga maniyyatan da ke son sauke farali a bana.

Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba An soma rigimar haraji tsakanin China da Amurka

Ana iya tuna cewa, da misalin ƙarfe goma sha biyun daren ranar Juma’a 31 ga watan Janairun 2025, ne wa’adin biyan kuɗin kujerun aikin hajjin bana ya cika.

Sai dai cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Hukumar NAHCON ta ƙasa, Fatima Sanda Usara ta fitar, ta ce tsawaita wa’adin wata dama ce ga maniyyatan da ba su kammala biyan kuɗin kujerar ba.

Hajiya Fatima ta kuma ce NAHCON ta buƙaci shugabannin hukumomin Alhazai na jihohi da su tabbatar sun bayar da haɗin kai na miƙa mata kuɗaɗen alhazan domin tanadar musu masauki a ƙasa mai tsarki.

Tun bayan cikar wa’adin na farko ne NAHCON, ta shaida wa BBC cewa, idan har akwai wani sabon bayani a game da ƙara wa’adin biyan kuɗin to hukumarsu za ta sanar.

NAHCON ta ce daga bayanan da suke samu daga jihohi kawo yanzu mutane sun biya kuɗinsu domin akwai ma waɗanda suka biya kuɗin da ya zarta wanda aka sanar sakamakon hasashen cewa kuɗin kujerar bana zai iya kai wa Naira miliyan 10.

“Yanzu irin waɗannan mutane da suka biya kuɗin da ya zarta na kujerar suna ta murna bayan sanar da kuɗin kujerar ta bana, kuma nan ba da jimawa ba za a mayar musu da sauran kuɗinsu bayan an cire wanda ya kamata,” in ji Hajiya Fatima.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kuɗin Kujera biyan kuɗin

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar

Fadar Shugaban Kasar Nijeriya, ta yi watsi da rahoton baya-bayan nan da kwamitin hulda da kasashen wajen Amurka ya fitar, wanda ya kafa hujja da amincewar majalisar dokokin kasar, na zargin kakaba wa wasu kiristoci takunkumi a kasar.

Mai bai wa shugaban kasa shawara a kan harkokin siyasa, Daniel Bwala, ya bayyana rahoton a matsayin wanda ba shi da tushe da makama, yana mai jaddada cewa; tun bayan lokacin da Shugaba Tinubu ya dare kan kujerar mulki a ranar 29 ga Mayun 2023, al’amuran cin zarafi, musamman ta fuskar addini suka yi matukar ja da baya.

Bwala, ya yi wannan furuci ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, wato na D; yana mai jaddada cewa, gwamnatinsu mai ci yanzu; ta himmatu wajen kokarin daidaita addinai a matsayin abu guda.

“Gwamnatin Bola Tinubu, koda-yaushe na kokarin bai wa addinai muhimmanci na musamman. Tun daga ranar 29 ga Mayun 2023, daidai lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya hau kan karagar mulki, ba a taba samun wasu matsaloli na tsananta wa Kiristoci a ko’ina a fadin wannan kasa ba”, kamar yadda ya rubuta.

Ya jaddada cewa, Nijeriya ta kasance kasa mai dauke da addinai daban-daban, sannan a kowane lokaci gwamnati na kokarin samar da zaman lafiya a tsakanin wadannan addinai.

Martanin da Fadar Shugaban Kasar ta mayar, ya biyo bayan nuna damuwa a kan matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta dauka na amincewa da takunkumin da aka kakaba wa Nijeriya, bisa zargin kashe Kiristoci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ko Raunin ‘Yan Wasa Zai Rage Wa Barcelona Karsashi A Kakar Bana?
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!
  • Wike Ya Kwace Filaye 4,794 A Abuja Saboda Rashin Biyan Kudin Ka’ida
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • Gwamnatin Bauchi Ta Ɗage Hawan Daushe Na Sallar Bana
  • Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai
  • Hajjin Bana: Maniyata 3, 155 Suka Yi Rijista a Kano
  • An Bukaci Shugaban Kasa Ya Sa Ido Ga Aikin Biyan Kudaden Fansho