Leadership News Hausa:
2025-03-25@17:53:18 GMT

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2 A Dajin Bauchi

Published: 5th, February 2025 GMT

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2 A Dajin Bauchi

Jami’an ‘yansanda tare da hadin gwiwar mafarauta sun kashe wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne a Dajin-madan, da ke karamar hukumar Alkaleri a jihar Bauchi. Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga wakilinmu a safiyar ranar Laraba, Kakakin Rundunar ’Yansandan Jihar Bauchi, CSP Ahmed Wakil, ya ce an kashe ‘yan bindigar ne ta hanyar amfani da bayanan sirri da hadin gwiwa da masu sa ido da ke cikin al’ummomin da abin ya shafa.

Tinubu Ya Amince Da Naira Biliyan 80 Domin Sake Gina Madatsar Ruwa Ta Alau Da Ke Borno Masana Kimiyyar Sin Sun Kirkiro Sabuwar Fasahar AI Mai Hasashen Zuwan Mahaukaciyar Guguwa Ya kara da cewa, bayan artabun, wasu daga cikin ‘yan bindigar sun tsere da raunukan harbin bindiga zuwa dazukan da ke kusa. Wakil ya ce, an kwato bindiga kirar AK-49 guda daya da harsashi guda tara daga hannun ‘yan ta’addan a yayin artabun.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24

Rahotanni daga Falasdinu na cewa akalla Falasdinawa 61 ne sukayi shahada a cikin sa’o’i 24 da suka gabata, in ji ma’aikatar lafiya ta Gaza.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, ma’aikatar ta ce an gano gawarwaki hudu a karkashin baraguzan gini, sannan an kwantar da mutane 134 da suka jikkata a asibiti cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

Adadin wadanda suka mutu a zirin Gaza ya kai 50,082, yayin da mutane 113,408 suka samu raunuka tun bayan fara yakin kisan kare dangi na Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Har ila yau, a ranar litinin, sojojin Isra’ila sun kai harin bam a asibitin Nasser, mafi girma a kudancin Gaza, da ke Khan Younis, harin da ma’aikatar ta yi Allah wadai da shi a matsayin “laifi na yaki.”

A ranar 1 ga Maris, bayan karewar kashi na farko na yarjejeniyar tsagaita bude wuta, Isra’ila ta kaurace wa shiga shawarwarin kashi na biyu na yarjejeniyar.

Tun a ranar 18 ga watan Maris ne dai aka sake tada jijiyoyin wuya, lokacin da Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare, lamarin da ya karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma musayar fursunoni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 2 Kan Zargin Kashe Ɗan Achaɓa Da Sace Babur Ɗinsa A Bauchi 
  • Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe
  • Ɗansanda Ya Kashe Matar Abokin Aikinsa, Ya Jikata Wasu Biyu A Ribas
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • An Kashe Askarawa 6 da ‘Yan Sa-kai 4 A Zamfara 
  • Karin Sinawa Suna Son Kashe Kudi
  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  
  • Matasa 4 Sun Yi Garkuwa Da Yaro, Sun Kashe Shi A Bauchi