NAHCON Ta Tsawaita Wa’adin Biyan Kuɗin Kujerar Aikin Hajjin 2025 zuwa 10 ga Fabrairu
Published: 5th, February 2025 GMT
Shugaban Hukumar jin dadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya sanar da tsawaita wa’adin biyan kudin kujerar aikin hajjin 2025 zuwa ranar 10 ga Fabrairu, 2025.
Karin wa’adin na zuwa ne biyo bayan koke-koke da aka kai wa hukumar na a kara wa maniyyatan da suka gaza kammala biyan kudinsu a kan lokaci.Nijeriya Na Iya Fuskantar Ƙarancin Maniyyata A Hajjin Bana EFCC Ta Gurfanar Da Manajan Darakta Kan Damfarar ₦144m A Gombe Farfesa Usman ne ya bayyana hakan a yayin wani taro da ya gudana a manhajar ‘Zoom’ a ranar Talata 4 ga watan Fabrairu, 2025, tare da masu ruwa da tsaki a shirye-shiryen gudanar da aikin Hajji. Shugaban Hukumar NAHCON ya yi kira ga Sakatarorin Zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jiha da su yi aiki tare da Hukumar don ganin an mika kudaden a kan lokaci, wanda ke da muhimmanci wajen tabbatar da biyan kudin masaukan da aka riga aka bincika kuma aka tanada.
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari
Kyari ya ci gaba da cewa, wannan bangare na noma don samun riba; shi ma zai amfana da Naira biliyan 500, wanda ya kai kimanin dala biliyan 300, wanda su ma wadannan kudaden za a bai wa Bankin Aikin na Noma.
Kazalika, Kyari ya yi kira ga Bankin EBRD, da ya zuba hannun jari a fannin aikin noman kasar, domin kasar ta cimma burin da ta sanya a gaba, musamman domin Nijeriya ta rage asarar da take yi a yayin girbin amfanin gona da samar da kayan aikin noman rani da sauran makamantansu.
Dakta Heike Harmgart, Manajan Daraknatan Bankin na EBRD da ke kula da yankin Afirka, wadda kuma ta jagoranci tawagar a nata jawabin ta ce, tawagar ta kawo ziyara ne ga Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci na kasar nan ne, sakamakon Nijeriya a kwanan baya ta zuba shaya ko hannun jari, domin gano bangarorin da ya kamata Bankin EBRD ya zuba hannun jarinsa a fannonin tattalin arzikin kasar.
Ta kara da cewa, Bankin na EBRD, zai yi aiki da Bankunan kasar nan; domin kara bunkasa zuba kudade a fannin aikin nomar kasar, inda ta ce; Bankin zai kuma bude ofishinsa a Jihar Legas.
“Muna kuma shirin daukar ‘yan Nijeriya masu hazaka, a bangarorin tattalin arzikin kasa, kuma a taron da za mu gudanar a watan Mayu na shekara-shekara, za mu gabatar da takardar bukata ga Nijeriya, kan bangarorin da za mu zuba hannun jari a kasar”, in ji Dakta Heike.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp